Shugabar jam’iyyar KMT(Kuomintang) ta kasar Sin, dake da hedkwata a yankin Taiwan na kasar Sin, Cheng Li-wun, ta isa birnin Shanghai a yau Talata tare da wata tawagar jami’ai, inda kuma ake sa ran bayan nan za su ziyarci birnin Nanjing.
Tun kama aiki a matsayin shugabar jam’iyyar KMT, Cheng Li-wun ta sha bayyana aniyarta ta ziyartar babban yankin kasar Sin. Kuma a yayin ziyarar ta wannan karo, ita da ’yan tawagarta za su kai ziyara a biranen Jiangsu, da Shanghai, da Beijing. (Saminu Alhassan)
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
ADVERTISEMENT















Discussion about this post