An kashe wasu ‘yan bindiga da dama a ranar Litinin bayan wata musayar wuta tsakanin sojoji da ‘yan ta’adda inda suka gudu, lokacin da ayarin motocin Babban Kwamandan Runduna (GOC) suka yi arangama da su a ƙaramar hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara.
Majiyoyin tsaro sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 4:30 na yammacin ranar Litinin, 6 ga Afrilu, 2026, yayin da GOC ke dawowa daga wata ziyarar aiki domin duba halin tsaro da kuma sojojin da aka jibge a Kulchin Kalgo da sansanin Forward Operating Base (FOB) da ke Danjibga.
- Sojoji Sun Kwato Yankuna, Sun Kashe Ƴan Bindiga 65 A Zamfara
- Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Zamfara
Rahotanni sun nuna cewa da ayarin motocin suka iso ƙauyen Maitashi, sun yi karo da ‘yan ta’adda suka gudu, lamarin da ya janyo musayar wuta tsakanin ɓangarorin biyu.
A yayin artabun, sojojin sun kashe wasu daga cikin maharan tare da kwato makamai da alburusai da babura.
Sai dai wani soja da ya samu raunukan harbin bindiga a lokacin artabun, an garzaya da shi zuwa cibiyar kula da lafiya ta Keta, inda daga bisani aka tabbatar da mutuwarsa.
Daga baya, sojojin sun share yankin kafin ayarin motocin su garzaya zuwa Gusau, babban birnin Jihar Zamfara, yayin da ake ci gaba da gudanar da ayyukan tsaro a yankin.















Discussion about this post