ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Siffofin Bahaushe A Shudadden Zamani Mai Nisa

by AUWAL ABDULLAHI SALISU
6 months ago
Bahaushe

Idan ba a manta ba, a makonni biyu da suka gabata a wannan shafin, mun ga asalin Kalmar zamantakewa da yadda take a yanzu a kuma magance . Sannan mun ga ma’anar Kalmar zamantakewa, da iren-irenta, haka zalika, mun ga ina ake kira da kasar Hausa a yau? Da yadda tsarin zaman Hausawa yake kama ga bambanci ta fuskar rukuni ko matsayin a zuzuwan al’ummar Hausawa.

Bahaushe A Jiya

Idan aka ce jiya ta kasu gida biyu akwai jiya ta nesa da kuma jiya ta kusa . Jiya ta nesa ita ce Jiyan da Bahaushe yake zaune a matsayin maras addini saukakke daga Allah (S.W.A), sai dai addini irin na tsarin zaman ‘yar marina, wato kowa gabansa, ma’ana kowa yana bautar abin da ya ga ya cancanci ya bautawa. Amma a lokacin da addinin musulunci ya zo kasar Hausa da yawa daga cikin Hausawa suka rungume shi a matsayiin addini  sabanin tsarin da suka taso suka tsinci  kansu a ciki na bantar dodanni ko gumakansu.

ADVERTISEMENT
  • Binciken CGTN: Babban Layin Dogo Na Sin Da Turai Wani Sabon Kuzari Ne Ga Budadden Tattalin Arzikin Duniya
  • Kasar Sin: Kashe Shugabanni Da Hare-Hare Kan Fararen Hula A Iran Abu Ne Da Ba Za A Lamunta Ba

Don haka, wadansu daga cikin su suka guji addinin Musulnci, da wannan ne wadancan bangare da suka karbi Musulunci suke kiran daya bangaren da suna maguzawa a matsayin jam’I amma a daidai ku Bamaguje, wato wanda ya guji addinin musulunci.

Amma idan muka ce nesa ta kusa ita ce, nesa da Bahaushe ya riga ya  ya karbi addinin musulunci, ya zama riga a gare shi wato, al-adunsa da dabi’unsa mafi akasari sun rikide sun zama na Musulunci.

LABARAI MASU NASABA

Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya

Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?

Don haka, a nan zamu kasa Hausawa da zamantakewarsu zuwa kashi uku, kamar haka:

Lokacin zama bai daya

Hausawa a zamanin Musulunci da maguzanci

Hausawa a zamanin Musulunci da zamantakewa  da dai-dai kun Maguzawa.

Hausawa a lokacin zama bai daya. A wancan lokacin zamantakewar Hausawa, Ita ake kira da zamantakewa bai daya tare da Hausawan dauri. A lokacin mutane ne wadanda suka fahimci zamaninsu, sannan suka san kansu. Mutane ne da suka riki  ababan bautarsu da gaskiya a wancan lokacin wanda tasirin hakan ya bayyana ta fuskar riko da addini a lokacin da Musulunci ya zo musu, sukai masa kyakkyawan riko. A wancan  lokacin akwai wadansu abubuwa wadanda Hausawa suka rike, a cikin tsarin zamantakewarsu wadanda su suka saya wa Bahaushe girma da daukaka a tsakanin makwabtansu da sauran kabilu abokan zamansu.

Manufar  rayuwa ga Bahaushen dauri ita ce a yi rayuwa ingantacciya cikin daraja da kaunar juna da kishin juna da taimakon juna. Bahaushe a wancan lokacin ya rike wadansu abubuwa  muhimmai wadanda su ne gishirin zaman duniya wato a cikin abin da ya shafi al’amuran rayuwarsu.

Wadannan abubuwan su suka sa rayuwar Bahaushe a da ta yi inganci. Bahaushen jiya mai nisa yana da tattali da  tsansteni da kulawa a al’amuransa na yau da kullum. Don haka ne ma yake  da wani a zancin Magana da yake    cewa kada-ran kada-han ma’ana kada-ka-ki-ci kada-ka cinye-duka, kuma komai zaka yi ka rinka sara-ka-na kallon bakin gatari. Bahaushe ya samu wannan falsafar ce domin shi kansa harshen Hausa a jiya mai nisa , harshe ne da yake cike da azanci da Karin Magana kuma azanci da  karin Magana, suna daga cikin abubuwan da ake amfani da su wajen auna  falsafar al’ummar duniya . Don haka za mu iya cewa, rayuwar Bahaushe a da cike take da falsafa wadda hakan ya kara taimaka masa cimma burace buracen rayuwa da ya sa a gaba.

Wadannan abubuwan suna daya daga cikin abubuwan da suka taka rawa wajen samun gida ko iyali na gari a cikin zamantakewar Bahaushe a zamanin dauri.

Siffofin Bahaushe A Zamanin Da Mai Nisa

Mutum ne mai takatsantsan kamar yadda muka ambata a baya, wannan taka  tsantsan din nasa ya shiga cikin ko wane bangare na rayuwarsa kuma ga neman aure yakan yi tattali dan gudun kada ya shiga tsaka  mai wuya          hakazalika, yana da kulawa wajen harkar iyalinsa da aikinsa da sauran al’umuran yau da kullum. Wadansu daga cikin sifoffin da Bahaushen da ya siffantu da su sun hada: tsare gaskiya da amana a dukkan al’amuransa, da zumunci da kana’a ko dangana da hakuri  game da halin da ya tsinci kansa ko ya tsinci kansa a halin rayuwa. Hakazalika, Bahaushe a da yana kiyaye dukkan wani abin da al’adarsa ta haramta masa ya aikata da kuma kawatawa cikin dukkan abin da al’adarsa ta halatta masa ya aikata, a takaice, za mu iya cewa, Bahaushe mutum ne mai kiyaye shari’a, sannan yana daga cikin siffofin Bahaushen da su ne, da’a ga manya ko jagorori a cikin al’umma.

Bahaushe mutum ne mai neman na kansa don haka nema yake da wata Karin Magana da take cewa a san mutum a san cinikinsa in ya bari a san ya  daina. Don haka nema Bahaushe yake da sana’o’in gargajiya kamar noma da kiwo da fatauci da kira da saka da jima  da dukanci da sasaka da kuma dori . A da ko ajiya musamman mai nisa za a tarar da Bahaushe  kwarare ne a kan sana’arsa.

Wata fitacciyar siffa da aka san Bahaushen dauri yake da ita , ita ce jaruntaka . Bahaushen da jarumi ne kuma yana  son jaruntaka, don haka ne ma yake zaune a sarari ba a cikin duhuwa ba,  wanda hakan yana daga cikin siffa ta jarumin mutum don haka Bahaushe bai san lalaci ba, ko ragwanci ko kuma matuwar zuciya ba.

Bahaushe
AUWAL ABDULLAHI SALISU
+ postsBio
    This author does not have any more posts.

MASU ALAKA

Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar
Bakon Marubuci

Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya

August 28, 2026
An Kusa Ceto Ɗaliban Neja Da Aka Sace – Ribadu
Bakon Marubuci

Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?

August 28, 2026
Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya
Bakon Marubuci

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

July 24, 2026
Next Post
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin

Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur'ani A Wannan Zamanin

LABARAI MASU NASABA

Bahaushe

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Bahaushe

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.