• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sigogin Tattalin Arzikin Kasar Sin Ba Su Sauya Ba

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Sigogin Tattalin Arzikin Kasar Sin Ba Su Sauya Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kakakin ma’ikatar harkokin wajen Sin Lin Jian, ya bayyana a yau Laraba cewa, sigogin tattalin arzikin kasar Sin da suka hada da tubali mai kwari da juriya mai karfi da tarin fifiko da kuzari mai yawa da kuma dimbin damarmaki, ba su sauya ba.

Hukumar kula da kididdiga ta kasar Sin ta fitar da bayanai game da yanayin tattalin arzikin kasar a rubu’in farko na bana, wadanda suka nuna cewa tattalin arzikin kasar na ci gaba da farfadowa kuma ya fara da kyakkyawan mafari. Sai dai, wasu kafafen yada labarai na yammacin duniya sun fi mayar da hankali kan wasu alkaluma marasa kuzari, inda suke shakku game da ko Sin za ta iya cimma burinta na samun habakar tattalin arzikin da kaso 5 a bana.

  • Idan Isra’ila Ta Kai Wa Iran Hari Ba Za Mu Goya Mata Baya Ba – Amurka
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Mata Da Yara, Sun Kashe Mai Unguwa A Wani Sabon Hari A Katsina

Da yake amsa tambayoyin manema labarai, Lin Jian ya bayyana cewa, bayanan da hukumar kula da kididdiga ta kasar ta fitar sun bayyana cewa, alkaluma da dama sun nuna cewa tattalin arzikin kasar na ci gaba da farfadowa, kuma ya samu kyakkyawan mafari a bana. A baya bayan nan, ana kara jin muryoyin daga kasa da kasa, wadanda ke bayyana kwarin gwiwarsu game da kasar Sin, da kuma tabbacin da suke da shi kan ci gaban kasar.

Da yake mayar da martani ga wasu kasashen yamma dake bayyana damuwa game da karfin masana’antun Sin na samar da kayayyaki fiye da kima, Lin Jian ya nanata cewa, ikirarin cewa wai samar da kayayyaki fiye da kima da kasar Sin ke yi na mummunan tasiri ga kasuwar duniya, ba shi da tushe, ya kamata batun ya dogara da ka’idojin tattalin arzikin kasuwa.

Kakakin ya kuma yi gargadin cewa, daukar matakan kariyar cinikayya, zai kawo tsaiko ga yanayi mai karko na sarrafawa da samar da kayayyaki, lamarin da zai lahanta kokarin raya tattalin arzikin duniya ba tare da gurbata muhalli ba da kuma ci gaban masana’antu masu tasowa.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Ya kara da cewa, masana’antun sabon makamashi na kasar Sin sun samu fifiko ne daga sahihiyar basira da isasshiyar takara a kasuwa, maimaikon rangwame daga gwamnati. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Sin: Tarihin Canton Fair Ya Nuna Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Fadada Bude Kofarta Ga Kasashen Waje

Next Post

Jami’an Tsaro sun Ceto Mata Biyu da aka Yi Garkuwa da Su A Kebbi

Related

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

12 hours ago
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

13 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

15 hours ago
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya
Daga Birnin Sin

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

16 hours ago
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
Daga Birnin Sin

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

17 hours ago
An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

18 hours ago
Next Post
Jami’an Tsaro sun Ceto Mata Biyu da aka Yi Garkuwa da Su A Kebbi

Jami'an Tsaro sun Ceto Mata Biyu da aka Yi Garkuwa da Su A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

July 12, 2025
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.