ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Jamus Suna Kokarin Hada Gwiwarsu Don Samarwa Duniya Tabbaci

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Sin

Kwanan nan, lokacin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugaban gwamnatin kasar Jamus Friedrich Merz a birnin Beijing, ya nuna cewa, kamata ya yi kasashensu biyu su karfafa tattaunawa bisa manyan tsare-tsare da kara amincewa da juna a siyasance, musamman a yayin da duniya ke fuskantar hali mai sarkakiya da sauye-sauye, ta yadda karfin dangantakar kasashen biyu zai kai ga samarwa duk fadin duniya tabbaci. Wannan furucin ba wai kawai ya nuna alkibla ga dangantakar Sin da Jamus a sabon zamani ba, har ma ya ba da tabbaci ga tsarin hadin gwiwar kasa da kasa, duba da kalubalen da ake fuskanta wajen tsarin jagorancin duniya.

A halin yanzu, ana fuskantar kunno kan ra’ayin bangaranci da nuna fin karfi a duniya, a yayin da kuma ake fuskantar kalubale ta fannin gudanar da harkokin kasa da kasa bisa tsarin dokokin duniya. Shugaba Xi ya sha jaddada cewa, ya kamata a kiyaye tsarin kasa da kasa bisa tushen MDD, da kuma kiyaye odar kasa da kasa bisa tushen tsarin dokokin duniya. A watan Satumba na shekara ta 2025, Xi ya gabatar da shawarar inganta tsarin shugabancin duniya, inda ya yi kira da a kiyaye daidaito tsakanin kasa da kasa wajen ikon mulkin kansu, da gudanar da harkokin duniya bisa tsarin dokokin kasa da kasa, da nacewa ga ra’ayin cudanyar mabambantan bangarori a duniya, kana da sanya moriyar jama’a a gaba da komai. Wannan shawara ta dace da yanayin zamani, har ma ta samu goyon bayan kasashe da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 150.

Ganawar shugabannin Sin da Jamus a wannan karo, ita ce misali mai kyau na tabbatar da ra’ayin kasancewar mabambantan bangarori a duniya. A yayin ganawarsu, shugaba Xi ya nuna cewa, ya kamata Sin da Jamus su mutunta matsayin MDD, da farfado da rawar jagoranci da MDD ke takawa, su kuma zama masu jagora a bangaren kiyaye ra’ayin cudanyar mabambantan bangarori a duniya, da aiwatar da dokokin kasa da kasa, da kare ciniki cikin ‘yanci. Kuma wannan ra’ayi ya samu amincewa daga bangaren Jamus.

ADVERTISEMENT

Hadin gwiwar kasuwanci da tattalin arzikin kasashen biyu shi ne muhimmin bangaren dangantakar Sin da Jamus, kuma muhimmancinsa ya wuce huldar kasashen biyu. Shugaba Xi a yayin ganawar, ya nuna cewa, bangarorin Sin da Jamus ya kamata su zama abokan hadin gwiwa na kirkire-kirkire da ke bude kofa ga juna da cin moriyar juna, kuma ya kamata bangarorin biyu su karfafa mu’ammala da juna ta fannin manufofin raya kansu, su inganta tattaunawa da hadin gwiwa a fagen fasahohin zamani kamar su fasahar AI da sauransu. Hakan ya samar da alkibla wajen zurfafa hadin gwiwar kasuwanci da tattalin arziki a tsakaninsu, kuma ya karawa tattalin arzikin duniya kwarin gwiwa da kuzari.

Dakatar da yaki da inganta zaman lafiya shi ne abin da aka sa gaba wajen inganta tsarin shugabancin duniya. Idan babu zaman lafiya, ta yaya za a yi magana game da tsarin shugabancin duniya? Bangarorin Sin da Jamus a cikin hadaddiyar sanarwarsu, sun ambaci batun Ukraine, inda suka nuna goyon bayan kokarin da ake yi na tsagaita bude wuta da kuma cimma zaman lafiya mai dorewa bisa kundin tsarin MDD.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Daga fitar da hadaddiyar sanarwa don kare ikon MDD, zuwa zurfafa hadin gwiwar kasuwanci don samar da sabon karfi ga tattalin arzikin duniya, Sin da Jamus sun sauke nauyin dake wuyan manyan kasashe bisa ainihin matakan da suke dauka. Kasashen biyu sun zabi tattaunawa maimakon warewa, hadin gwiwa maimakon katse huldar tattalin arziki, cudanyar mabambantan bangarori maimakon ra’ayin bangaranci, yayin da ake fuskantar hadarin rarrabuwar kawuna da adawa da juna, wannan shi ne tabbacin da duniya mai fuskantar rashin hankali take matukar bukata, kuma shi ne hakikanan matakan da ake dauka wajen tabbatar da tsarin shugabancin duniya. (Marubuci: MINA)

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 2

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 10

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.