ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Jamus Suna Kokarin Hada Gwiwarsu Don Samarwa Duniya Tabbaci

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Sin

Kwanan nan, lokacin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugaban gwamnatin kasar Jamus Friedrich Merz a birnin Beijing, ya nuna cewa, kamata ya yi kasashensu biyu su karfafa tattaunawa bisa manyan tsare-tsare da kara amincewa da juna a siyasance, musamman a yayin da duniya ke fuskantar hali mai sarkakiya da sauye-sauye, ta yadda karfin dangantakar kasashen biyu zai kai ga samarwa duk fadin duniya tabbaci. Wannan furucin ba wai kawai ya nuna alkibla ga dangantakar Sin da Jamus a sabon zamani ba, har ma ya ba da tabbaci ga tsarin hadin gwiwar kasa da kasa, duba da kalubalen da ake fuskanta wajen tsarin jagorancin duniya.

A halin yanzu, ana fuskantar kunno kan ra’ayin bangaranci da nuna fin karfi a duniya, a yayin da kuma ake fuskantar kalubale ta fannin gudanar da harkokin kasa da kasa bisa tsarin dokokin duniya. Shugaba Xi ya sha jaddada cewa, ya kamata a kiyaye tsarin kasa da kasa bisa tushen MDD, da kuma kiyaye odar kasa da kasa bisa tushen tsarin dokokin duniya. A watan Satumba na shekara ta 2025, Xi ya gabatar da shawarar inganta tsarin shugabancin duniya, inda ya yi kira da a kiyaye daidaito tsakanin kasa da kasa wajen ikon mulkin kansu, da gudanar da harkokin duniya bisa tsarin dokokin kasa da kasa, da nacewa ga ra’ayin cudanyar mabambantan bangarori a duniya, kana da sanya moriyar jama’a a gaba da komai. Wannan shawara ta dace da yanayin zamani, har ma ta samu goyon bayan kasashe da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 150.

Ganawar shugabannin Sin da Jamus a wannan karo, ita ce misali mai kyau na tabbatar da ra’ayin kasancewar mabambantan bangarori a duniya. A yayin ganawarsu, shugaba Xi ya nuna cewa, ya kamata Sin da Jamus su mutunta matsayin MDD, da farfado da rawar jagoranci da MDD ke takawa, su kuma zama masu jagora a bangaren kiyaye ra’ayin cudanyar mabambantan bangarori a duniya, da aiwatar da dokokin kasa da kasa, da kare ciniki cikin ‘yanci. Kuma wannan ra’ayi ya samu amincewa daga bangaren Jamus.

ADVERTISEMENT

Hadin gwiwar kasuwanci da tattalin arzikin kasashen biyu shi ne muhimmin bangaren dangantakar Sin da Jamus, kuma muhimmancinsa ya wuce huldar kasashen biyu. Shugaba Xi a yayin ganawar, ya nuna cewa, bangarorin Sin da Jamus ya kamata su zama abokan hadin gwiwa na kirkire-kirkire da ke bude kofa ga juna da cin moriyar juna, kuma ya kamata bangarorin biyu su karfafa mu’ammala da juna ta fannin manufofin raya kansu, su inganta tattaunawa da hadin gwiwa a fagen fasahohin zamani kamar su fasahar AI da sauransu. Hakan ya samar da alkibla wajen zurfafa hadin gwiwar kasuwanci da tattalin arziki a tsakaninsu, kuma ya karawa tattalin arzikin duniya kwarin gwiwa da kuzari.

Dakatar da yaki da inganta zaman lafiya shi ne abin da aka sa gaba wajen inganta tsarin shugabancin duniya. Idan babu zaman lafiya, ta yaya za a yi magana game da tsarin shugabancin duniya? Bangarorin Sin da Jamus a cikin hadaddiyar sanarwarsu, sun ambaci batun Ukraine, inda suka nuna goyon bayan kokarin da ake yi na tsagaita bude wuta da kuma cimma zaman lafiya mai dorewa bisa kundin tsarin MDD.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Daga fitar da hadaddiyar sanarwa don kare ikon MDD, zuwa zurfafa hadin gwiwar kasuwanci don samar da sabon karfi ga tattalin arzikin duniya, Sin da Jamus sun sauke nauyin dake wuyan manyan kasashe bisa ainihin matakan da suke dauka. Kasashen biyu sun zabi tattaunawa maimakon warewa, hadin gwiwa maimakon katse huldar tattalin arziki, cudanyar mabambantan bangarori maimakon ra’ayin bangaranci, yayin da ake fuskantar hadarin rarrabuwar kawuna da adawa da juna, wannan shi ne tabbacin da duniya mai fuskantar rashin hankali take matukar bukata, kuma shi ne hakikanan matakan da ake dauka wajen tabbatar da tsarin shugabancin duniya. (Marubuci: MINA)

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 2

Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 10

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.