Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau Alhamis, cewa game da batun cika shekaru 30 tun bayan da Sin ta sanar da dakatar da gwajin nukiliya, kasar na kan bakanta na wanzar da manufofin nukiliya bisa hangen nesa a dogon lokaci, tana kuma ci gaba da kiran hanawa, har ma da lalata dukkan makaman nukiliya. Kazalika, Sin ta sanar da cewa, ba za ta yi amfani da makaman nukiliya da farko ba, kana ta sha alwashin kin amfani da makaman nukiliya kan kasashe da yankunan da ba su mallaki makaman nukiliya ba.
Ranar 30 ga watan Yuli, rana ce ta cika shekaru 27 da daddale takardar fahimtar juna a tsakanin gwamnatin Sin da ta Japan, game da lalata makamai masu guba da kasar Japan ta ajiye a cikin kasar Sin. Kuma dangane da hakan, Mao Ning ta bayyana cewa, lalata dukkan makamai masu guba na kasar Japan dake kasar Sin, alhaki ne na kasar Japan a fannonin tarihi, da siyasa da kuma martaba dokoki.
Game da kiran da ministan harkokin wajen kasar New Zealand Winston Peters ya yi, cewa wani dan majalisar dokokin kasar dan asalin kasar Sin ya koma kasarsa, Mao Ning ta bayyana cewa, kasar Sin ba za ta amince da duk wani mataki na nuna bambancin launin fata ba. (Zainab Zhang)














