Bangaren kasar Sin ya yi bayani kan matsayinsa dangane da hana yaduwar makaman nukiliya a gun taron bincike da tattaunawa kan yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya karo na 11 da aka gudanar jiya, a cibiyar MDD dake birnin New York. Bangaren Sin ya yi nuni da cewa, wasu kasashe sun dauki ma’auni biyu kan batun hana yaduwar makaman nukiliya, kuma hakan yana rage karfin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya da tsarin sa ido na hukumar makamashin nukiliya ta duniya IAEA.
Kasar Sin ta ce, kasar Japan tana yunkuri maras dacewa kan batun mallakar makaman nukiliya a shekarun baya-baya nan, don haka ya kamata kasa da kasa su maida hankali kan wannan batu.Jakadan Sin mai kula da rage yawan makaman soja Shen Jian ya bayyana a gun taron cewa, ya kamata a rage rawar da makaman nukiliya ke takawa a cikin manufofin tsaron kasa.
Ya ce, kasar Sin na adawa da yaduwar makaman nukiliya, kuma tana kira da bin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya a dukkan fannoni yadda ya kamata, haka kuma tana son hada hannu da kasa da kasa don tabbatar da tsarin hana yaduwar makaman nukiliya bisa tushen yarjejeniyar. (Zainab Zhang)















Discussion about this post