ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sirrin Kasar Sin Na Fitar Da Al’ummunta Daga Kangin Talauci

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Sin

A kwanakin nan, wata jami’a da ke kula da ayyukan tallata amfanin gona ta jihar Xinjiang da ke arewa masu yammacin kasar Sin ta rasu sakamakon mummunan raunin da ta ji a sanadin fadowarta daga doki, a lokacin da take daukar shirin bidiyo na tallata amfanin gona, lamarin ya janyo hankalin al’ummar kasar Sin sosai, kuma masu bibiyar shafinta da yawa sun yi ta rubuta kalamai na jimami a hotunan bidiyon da ta wallafa, inda suka ce, “Ke ce kika fahimtar da al’ummun kasar Sin game da gundumar Zhaosu, har da yankin Yili da ma kykkyawar jihar Xinjiang baki daya.” “Sakamakon kokarinki, rayuwar manoma da makiyaya ta kyautata”.

Sunan jami’ar shi ne He Jiaolong. A shekarar 2020, malama He Jiaolong wadda a lokacin ke kan kujerar mataimakiyar shugaban gundumar Zhaosu, ta fara tallata amfanin gona na wurin ta shafinta na sada zumunta. A daidai waccan shekara kuma, wani hoton bidiyon da ta dauka game da yadda take hawan doki da ke gudu a filin da dusar kankara ta rufe, sanye da jar riga, ya yi matukar samun farin jini daga masu ziyartar shafukan yanar gizo, lamarin da ya sa ta yi suna, har ma gundumar Zhaosu ta fara janyo hankalin al’umma. A shekarar 2021, yawan baki masu yawon shakatawa da ke zuwa gundumar Zhaosu ya ninka na baya har sau da dama.

Duk da haka, malama He Jiaolong ba ta taba kallon kanta a matsayin tauraruwa ba. Ta ce, burinta shi ne fatan ganin masu bibiyar shafinta za su fara mayar da hankalinsu a kan gundumar Zhaosu bisa hotunan bidiyon da ta wallafa, don janyo karin baki masu yawon shakatawa tare da sayar da amfanin gona na gundumar zuwa sassa daban daban na kasar Sin. Sau da yawa malama He Jiaolong ta ce, “Yadda aka ilmantar da mu, ba don mu fita daga garuruwanmu da ke fama da talauci ba ne, sai dai don mu yi kokarin fitar da garuruwan daga kangin talauci da suke ciki.”

ADVERTISEMENT

Jihar Xinjiang yanki ne da Allah ya albarkace shi da ni’imtaccen yanayi da ma wadatattun amfanin gona. A cikin ’yan shekarun baya, malama He Jiaolong ta dukufa wajen yayata al’adu da gabatar da bayanan da suka shafi wuraren yawon shakatawa na jihar, da ma tallata amfanin gona na wurin. Tun daga shekarar 2020, malama He Jiaolong tare da sauran ma’aikata da ke tallafa mata, sun yi ta tallata amfanin gona na jihar Xinjiang ba tare da samun ladan aikin ba, don taimaka wa manoma sayar da amfaninsu, matakin da kuma ya samar da karin guraben aikin yi ga al’ummar wurin. Daga shekarar 2021 har zuwa 2024, malama He Jiaolong ta wallafa hotunan bidiyo 628, tare da gudanar da tallan kayayyakin amfanin gona ta bidiyo kai tsaye har sau 396, inda kudin cinikin da aka yi bisa tallar ta ya kai Yuan miliyan 360, kwatankwacin dala kimanin miliyan 52. Shafinta ya yi ta tattara kayayyaki masu inganci na sassan jihar Xinjiang, tare da sayar da su zuwa sassa daban daban na kasar Sin, matakin da ya samar da karin kudin shiga ga manoma da ma karin guraben aikin yi ga al’ummar yankin.

A karshen shekarar 2020, kasar Sin ta cimma burin da ta sanya gaba na saukaka fatara, inda aka fitar da al’ummu kimanin miliyan 989.9 da ke yankunan karkara, da gundumomi 832, da kuma kauyuka dubu 128 daga kangin talaucin da suke ciki, shekaru 10 ke nan kafin a cimma burin saukaka fatara na MDD, bisa ajandarta ta tabbatar da dauwamammen ci gaba ta zuwa shekarar 2030. A lokacin, akwai abokaina ’yan Afirka da suka min tambaya, shin ta yaya kasar Sin ta cimma wannan gagarumar nasara? A ganina, hakan ya tabbata ne sakamakon kokarin da aka yi ta fannoni da dama, kuma ba shakka, jami’ai a mataki na farko irinsu malama He Jiaolong sun ba da babbar gudummawa.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Raya sassa daban daban bisa mabambantan yanayin da suke ciki, da kuma kirkire-kirkire su ne bakin zaren warware matsalar tabbatar da ci gabansu, kuma muna iya gano hakan ne daga yadda gundumar Zhaosu ta dogara ga ni’imtaccen yanayi, da ma albarkatun dabbobin kiwo da take da su wajen raya sana’o’i na musamman, da ma yadda malama He Jiaolong ta yi kirkire-kirkire wajen tallata amfanin gona na wurin.

Malama He Jiaolong ta rasu, amma ruhinta zai dore. Domin jama’a ake saukakawa fatara, kuma ana dogara ga jama’a wajen saukaka fatara, baya ga haka, rikon gaskiya da raya sassa daban daban bisa mabambantan yanayin da suke ciki, duk wadannan sun kasance dabarar kasar Sin wajen saukaka fatara, wanda hakan zai haskakawa kasashen duniya hanyar fitar da kansu daga talauci.

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Yadda Ake Zama Da Uwar Miji  (2)

Yadda Ake Zama Da Uwar Miji  (2)

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.