Dakarun Sojin Nijeriya sun samu wata gagarumar nasara wajen ceto mutane shida da masu garkuwa da mutane suka sace, tare da ƙwato kuɗi har Naira 800,000 daga hannun ɓata-gari a wani sumame da suka kai a Jihar Katsina. Wannan namijin ƙoƙarin yana daga cikin ayyukan daƙile ta’addanci da sojojin ke ci gaba da gudanarwa a yankin Arewa maso Yamma don tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.
A cewar wata majiyar tsaro, sojojin sun kai farmakin ne bayan samun bayanan sirri game da maɓoyar ƴan bindigar, inda suka yi musayar wuta kafin daga bisani su fatattake su. An bayyana cewa waɗanda aka ceto ɗin sun haɗa da mata da maza waɗanda aka sace daga garuruwansu, kuma tuni aka miƙa su ga iyalansu bayan an duba lafiyarsu don tabbatar da cewa suna cikin yanayi mai kyau.
Baya ga mutanen da aka ceto da kuma maƙudan kuɗaɗen da aka ƙwato, dakarun sun kuma lalata sansanonin ‘yan ta’addan sannan suka kwace wasu makamai da harsasai da bata-garin ke amfani da su wajen cin zarafin al’umma. Majiyar ta ƙara da cewa wannan aiki ya nuna kwazon dakarun tsaro wajen ganin an yi maganin duk wata barazana da ta dabaibaye yankunan karkara a jihar.
Al’ummar Jihar Katsina sun yi maraba da wannan ci gaba, inda suka buƙaci a ci gaba da kai irin waɗannan farmakin ba-zata har sai an raba jihar da duk wani gurbataccen mutum da ke neman tayar da zaune tsaye ko hana manoma zuwa gonakinsu. Wannan nasara dai na ƙara ƙarfafa gwuiwar ƴan ƙasa game da aniyar jami’an tsaro na kawo ƙarshen matsalar garkuwa da mutane da fashin daji.














