Dakarun Sojin Nijeriya a Jihar Taraba sun kama mutane biyu da ake zargi da safarar makamai ba bisa ƙa’ida ba, a wani samame da aka gudanar bisa sahihan bayanan sirri.
An kama wanda ake zargi na farko, Christopher Adamu, a Jalingo, yayin da aka kama na biyu, James Yangyang, daga bisani a yankin Ardo Kola na jihar.
- ‘Yan Ta’adda 11 Sun Miƙa Wuya Yayin Da Sojoji Suka Kashe 8 A Borno
- Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)
Sojojin sun bayyana cewa bincike ya nuna mutanen biyu na cikin wata ƙungiya da ke safarar makamai da kuma rarraba su a wasu sassan jihar.
Daga cikin abubuwan da aka ƙwato a yayin aikin akwai katin shaida, katin ATM, wayar hannu da kuma wasu kayan tsafi.
Bincike ya kuma gano cewa ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin ya sayar da bindiga ƙirar AK-47 ga wani mutum a watan Nuwamban 2025, lamarin da ya tabbatar da safarar makamai a yankin.
A halin yanzu, mutanen biyu suna hannun sojoji domin ci gaba da bincike, kafin a miƙa su ga hukumomin da suka dace domin gurfanar da su a gaban kotu.
Sojojin sun kuma yi gargaɗi ga masu aikata laifuka da masu safarar makamai da su guji Jihar Taraba, tare da kira ga al’umma su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai.















Discussion about this post