Dakarun Rundunar Sojojin “Operation haɗin kai” waɗanda ke aiki a ƙarƙashin shirin “desert sanitY”, sun samu nasar kashe ‘yan ta’adda, tare da ceto mutanen da aka sace haɗi ida kwato makamai da harsasai da abubuwan fashewa.
Wannan na cikin Wata sanarwa da Laftanar Kanar Sani Uba, Jami’in Yaɗa Labarai na shalƙwatar Rundunar ta Operation haɗin kai, ya fitar a ranar Asabar.
Sanarwa ta ce “An samu nasarar samun ababen fashewa tare da lalata su da kuma ɗaukar waɗanda ba akai ga haɗa su ba, sannan sojojin suka sami nasarar kama wasu daga cikin makaman ‘yan ta’addan da suka kashe da kuma ceto wasu mutane da aka sace domin yin garkuwa da su”
Tun da fari dai Uba ya ce “Sojojin Rundunar sun yi karan batta da mayaƙan ISWAP/ Boko Haram a yankin Ngoshe inda dakurun sojojin suka yi nasarar kashewa tare da kama sauran kayayyakin da suka bari”
Haka zalika sanarwa ta ƙara da cewa sojojin sun sami nasarar fattatakan wasu daga cikin ‘yan ta’addan a yankin Buni Gari in da nan ma suka samu gaggarumar nasara.
Daga ƙarshe sanarwa ta yabawa dakarun sojojin bisa ƙwarewa da dagewar su wajen tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa.















Discussion about this post