Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ce ta amince da wannan mataki, inda ta bayar da umarnin a fara bincikar tsohuwar gwamnatin Muhammad Badaru Abubakar.
Hakan ya biyo bayan amincewa da rahoton Kwamitin Asusun Jama’a na Majalisar, wanda ya gudanar da cikakken bincike kan harkokin kuɗaɗen ma’aikatu.
Yayin gabatar da rahoton a zaman majalisar, shugaban kwamitin, Isyaku Abubakar, ya bayyana cewa binciken ya samo asali ne daga rahotannin ofisoshin Babban Mai Binciken Kuɗi na Jiha da kuma na ƙananan hukumomi. Haka kuma, an gudanar da sauraron ra’ayoyin jama’a tare da halartar manyan jami’an gwamnati.
Ya ƙara da cewa, an gayyaci kwamishinoni, manyan sakatarori, daraktocin kuɗi da kuma shugabannin ƙananan hukumomi domin su yi ƙarin bayani kan wasu kuɗaɗe. Kwamitin ya kuma tabbatar da cewa an bi duk ƙa’idoji a tsawon lokacin gudanar da aikin.
Rahoton ya nuna wasu matsaloli da suka haɗa da rashin cikakkun takardu, saɓani a bayanan kashe kuɗi, da kuma rauni a tsarin sa ido a matakin jiha da kuma ƙananan hukumomi.















Discussion about this post