• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe ‘yan Ta’addar Iswap Da Dama A Yobe Yayin Da Jami’in CJTF 1 Ya Mutu A Borno

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
‘Yan Ta’adda Da Dama Sun Mutu A Wata Arangama Tsakanin ISWAP Da Boko Haram A Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dakarun Sojojin Nijeriya sun yi ruwan bama-bamai a sansanin ‘yan ta’addar Daesh a yankin Yammacin Afirka (ISWAP), inda suka kashe ‘yan ta’adda da dama a jihar Yobe.

LEADERSHIP ta rawaito cewa, ‘yan ta’addar sun hadu ne akan babura sun nufi wurin da niyyar kai hari a sansanin Soji.

  • ISWAP Ta Sace Jami’an Tsaro 7 A Borno
  • Da Dumi-dumi: Mayakan ISWAP Sun Kai Wa ‘Yan Boko Haram Farmaki

Wani rahoton sirri da Zagazola Makama, kwararre a fannin yaki da tada kayar baya a yankin tafkin Chadi ya samu daga manyan majiyoyin soji, wanda ya samu wakilinmu, ya nuna cewa, a bisa bayanan sirri, sojojin bataliya ta 27 Task Force Battalion, sun harba makaman atilare da dama. ‘yan ta’addar da suka yi sanadiyar kashe mutanen da ba a tantance adadinsu ba.

An kuma bayyana cewa daga baya ‘yan ta’addar sun dawo a kan babura 6 da mota daya domin kwashe gawarwakinsu.

A wani labarin kuma, wani jami’in ‘Civilian Joint Task Force’ (CJTF) ya rasa ransa yayin da wasu 4 suka jikkata a wani samame da ‘yan ta’addan ISWAP suka kai da tsakar dare a kauyen Benisheik da ke karamar hukumar Kaga a jihar Borno.

Labarai Masu Nasaba

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Kotu Ta Yanke Wa ÆŠan TikTok Tsulange Hukuncin ÆŠauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Benisheikh yana da nisan kilomita 72 da nisan mil 44.8 zuwa Maiduguri babban birnin jihar Borno.

An rawaito cewa ‘yan ta’addan sun kutsa cikin garin ne a kan babura da misalin karfe 3:30 na safe inda suka yi artabu da jami’an tsaro.

Wani rahoton leken asirin da Zagazola Makama ya samu ya ce ‘yan ta’addar sun yi galaba a kan jami’an tsaro, inda suka kashe daya daga cikinsu da kona motocin sintiri hudu.

Majiyar ta bayyana cewa ‘yan ta’addar sun ja da baya inda suka yi taho-mu-gama a lokacin da suka hango wata tawaga ta hadin gwiwa da sojojin Nijeriya.

Idan dai za a iya tunawa, Makama ya yi gargadin cewa ‘yan ta’addar na shirin kai hare-hare da dama a wasu wurare a fadin kasar nan tsakanin Satumba da Oktoba, 2022.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shahararren Malamin Addinin Musulunci, Youssef Al- Qaradawi Ya Rasu

Next Post

Kasar Sin Ta Samu Nasarori A Bangaren Ginin Ababen More Rayuwa Na Zamani

Related

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

8 hours ago
Kotu Ta Yanke Wa ÆŠan TikTok Tsulange Hukuncin ÆŠauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci
Labarai

Kotu Ta Yanke Wa ÆŠan TikTok Tsulange Hukuncin ÆŠauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

9 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku

9 hours ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

10 hours ago
Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue
Labarai

Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

11 hours ago
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
Manyan Labarai

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

13 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Samu Nasarori A Bangaren Ginin Ababen More Rayuwa Na Zamani

Kasar Sin Ta Samu Nasarori A Bangaren Ginin Ababen More Rayuwa Na Zamani

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa ÆŠan TikTok Tsulange Hukuncin ÆŠauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa ÆŠan TikTok Tsulange Hukuncin ÆŠauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.