ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Tarwatsa Gungun Masu Tayar Da Bam A Adamawa

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
Sojoji

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Rundunar Sojojin Nijeriya na atisayen haɗin kai (OPHK) ta tarwatsa wata ƙungiyar masu shirya harin bam na ƙunar baƙin wake tare da daƙile hanyoyin jigilar kayayyakin ‘yan ta’addan Boko Haram/ISWAP a Jihar Adamawa. Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na rundunar, Laftanar Kanar Sani Uba, ya fitar a Maiduguri ranar Litinin.

Sanarwar ta ce dakarun OPHK sun samu gagarumar nasarar ne yayin ci gaba da aiyukan kewaye da bincike da ake yi domin gano masu hannu a harin bam da aka kai Masallacin Kasuwar Gamboru a jajibirin Kirsimeti a Maiduguri. Biyo bayan sa ido na tsanaki kan wasu wurare, Sojojin sun kai sumame a unguwar Ƴan Lemo da ke Ƙaramar Hukumar Mubi ta Kudu a safiyar 5 ga Janairu, 2026.

  • Bayan Taka Nakiya, Sojoji 9 Sun Rasu, Wasu Sun Raunata A Borno
  • Gwamnatin Adamawa Ta Sanya Dokar Hana Fita Daga Lamurde Na Sa’o’i 24

A yayin sumamen, an kama mutane takwas da ake zargi, ciki har da manyan mutane biyu da ake zaton su ne ke jagorantar hanyar samar da kayan harin bam. Binciken da aka yi a gidajensu ya haifar da gano kuɗi, da wayoyin hannu, da takardun shaida, da katinan ATM, da kayan ado da sauran kayayyaki, waɗanda ake ci gaba da tantancewa domin tallafa wa binciken da ake yi. Wani wanda ke tsare a baya ya tabbatar da cewa manyan waɗanda aka kama su ne suka samar da kayayyakin haɗa bam ɗin IED.

ADVERTISEMENT

A wani ɓangare na aikin, rundunar ta OPHK ta kama wani kayan man fetur da ake zargin an tanade shi ne domin ƴan ta’adda a garin Mayo Nguli da ke ƙaramar Hukumar Maiha a ranar 4 ga Janairu, 2026. Sojojin sun kwace jarkoki 45 na man fetur mai lita kimanin 1,125, bayan da masu safarar suka tsere suka bar kayan. Rundunar ta jaddada ƙudirinta na murƙushe hanyoyin ƴan ta’adda, tare da kira ga jama’a da su kasance masu sa ido da haɗin kai da hukumomin tsaro domin tabbatar da ɗorewar tsaro a yankin Arewa maso Gabas.

Sojoji
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
AFCON 2025: Super Eagles Sun Murƙushe Mozambique Da Ci 4–0

AFCON 2025: Super Eagles Sun Murƙushe Mozambique Da Ci 4–0

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.