ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Tarwatsa Gungun Masu Tayar Da Bam A Adamawa

by Abubakar Sulaiman
6 months ago
Sojoji

LABARAI MASU NASABA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Rundunar Sojojin Nijeriya na atisayen haɗin kai (OPHK) ta tarwatsa wata ƙungiyar masu shirya harin bam na ƙunar baƙin wake tare da daƙile hanyoyin jigilar kayayyakin ‘yan ta’addan Boko Haram/ISWAP a Jihar Adamawa. Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na rundunar, Laftanar Kanar Sani Uba, ya fitar a Maiduguri ranar Litinin.

Sanarwar ta ce dakarun OPHK sun samu gagarumar nasarar ne yayin ci gaba da aiyukan kewaye da bincike da ake yi domin gano masu hannu a harin bam da aka kai Masallacin Kasuwar Gamboru a jajibirin Kirsimeti a Maiduguri. Biyo bayan sa ido na tsanaki kan wasu wurare, Sojojin sun kai sumame a unguwar Ƴan Lemo da ke Ƙaramar Hukumar Mubi ta Kudu a safiyar 5 ga Janairu, 2026.

  • Bayan Taka Nakiya, Sojoji 9 Sun Rasu, Wasu Sun Raunata A Borno
  • Gwamnatin Adamawa Ta Sanya Dokar Hana Fita Daga Lamurde Na Sa’o’i 24

A yayin sumamen, an kama mutane takwas da ake zargi, ciki har da manyan mutane biyu da ake zaton su ne ke jagorantar hanyar samar da kayan harin bam. Binciken da aka yi a gidajensu ya haifar da gano kuɗi, da wayoyin hannu, da takardun shaida, da katinan ATM, da kayan ado da sauran kayayyaki, waɗanda ake ci gaba da tantancewa domin tallafa wa binciken da ake yi. Wani wanda ke tsare a baya ya tabbatar da cewa manyan waɗanda aka kama su ne suka samar da kayayyakin haɗa bam ɗin IED.

ADVERTISEMENT

A wani ɓangare na aikin, rundunar ta OPHK ta kama wani kayan man fetur da ake zargin an tanade shi ne domin ƴan ta’adda a garin Mayo Nguli da ke ƙaramar Hukumar Maiha a ranar 4 ga Janairu, 2026. Sojojin sun kwace jarkoki 45 na man fetur mai lita kimanin 1,125, bayan da masu safarar suka tsere suka bar kayan. Rundunar ta jaddada ƙudirinta na murƙushe hanyoyin ƴan ta’adda, tare da kira ga jama’a da su kasance masu sa ido da haɗin kai da hukumomin tsaro domin tabbatar da ɗorewar tsaro a yankin Arewa maso Gabas.

Sojoji
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
  • Abubakar Sulaiman
    An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15
  • Abubakar Sulaiman
    Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

MASU ALAKA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
Rahotonni

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
Labarai

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
Labarai

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
Next Post
AFCON 2025: Super Eagles Sun Murƙushe Mozambique Da Ci 4–0

AFCON 2025: Super Eagles Sun Murƙushe Mozambique Da Ci 4–0

LABARAI MASU NASABA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.