Rahotanni daga Jihar Borno sun ce wani harin da Dakarun Sojin Nijeriya suka kai bisa kuskure ya yi sanadin mutuwar mutanen gari da dama.
An ce harin ya faru ne a ranar 14 ga watan Disamba a yankin Mararraba da ke Ƙaramar Hukumar Kukawa.
- Tsohon Alƙalin Alƙalan Nijeriya, Ibrahim Tanko Muhammad, Ya Rasu
- Gobara Ta Ƙone Ginin Da Ake Danganta Wa Tsohon Gwamnan Zamfara, Ahmed Yerima, A Abuja
Sojojin saman sun yi luguden wuta ne da nufin kai wa ’yan ta’adda hari, amma suka afkawa masunta da direbobin motoci da ke safarar kifi.
Wasu da suka tsira daga harin sun ce aƙalla motoci 10 ne suka lalace, sannan mutane da dama sun mutu da kuma jikkata.
Waɗanda suka ji rauni suna karɓar magani a babban asibitin Munguno.
Bayanai sun nuna cewa jiragen yaƙin sun yi ta harbi daga karfe 6 na safe zuwa kusan 4 na yamma.
Lamarin ya faru ne bayan Sojin Saman Nijeriya sun sha alwashin kare fararen hula tare da ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ’yan ta’adda.














