Gobara ta tashi a wani gini da ake zargin mallakar tsohon gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Ahmed Sani Yerima ne a unguwar Asokoro da ke Abuja, inda ta lalata ɗakuna huɗu cikin biyar na gidajen kwana masu ɗakuna uku-uku.
Lamarin ya faru ne a ranar Asabar da misalin ƙarfe 1 na rana a gini mai lamba 13, titin Nelson Mandela, inda bidiyoyi da suka yaɗu a kafafen sada zumunta suka nuna hayaƙi mai yawa da wutar da ke tashi yayin da jami’an kashe gobara ke ƙoƙarin shawo kanta.
- Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda
- Dawo Da Martabar Birnin Abuja Ta Hanyar Doka Da Oda Shi Ne Babbar Burin Wike – Mukthar Galadima
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Birnin Tarayya (FEMD) ta tabbatar da aukuwar lamarin, inda ta ce babu asarar rai, sai dai gobarar ta lalata kayan ɗaki, da tufafi, da abinci da sauran kayayyakin mazauna gidajen da abin ya shafa.
Rahotannin da aka fara samu sun nuna cewa gobarar na iya samo asali ne daga na’urar samar da wutar lantarki ta hasken rana (solar), yayin da jami’an FEMD, da Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya, da NEMA da jami’an ƴansanda suka haɗa ƙarfi wajen daƙile yaɗuwar wutar.














