ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Hanyar Kyautata Fasahar Makamashi Kasar Sin Na Samar Da Damar Raya Kasa Ga Sauran Kasashe

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 months ago

A duniyarmu, akwai kasar da ta kan ambaci burinta na sake zama wata kasa mai karfi. Sai dai mai karfi ba ya nufin wanda za a iya ta da rikici a duniya, ko kuma cin zarafin sauran kasashe yadda ya ga dama.

Hakika karfin wata kasa yana bayyana ne kawai ta hanyar kiyaye wani yanayi na ci gaban tattalin arzikinta, gami da raba damar ci gaba tare da sauran kasashe, a lokacin da ake fama da yanayin rashin tabbas da kwanciyar hankali a duniya.

A kwanakin nan, kasar Sin ta sanar da alkaluman tattalin arzikinta a rubu’in farko na bana, wadanda suka nuna cewa, jimillar GDPn kasar ta karu da kaso 5% idan an kwatanta da jimilla ta makamancin lokacin shekarar bara, inda ta kai wani matsayi na koli bisa burin karuwar GDP da kasar ke neman samu a shekarar 2026, wato tsakanin 4.5% da 5%.

ADVERTISEMENT

Sai dai ta yaya kasar Sin ta tabbatar da karuwar tattalin arzikinta cikin sauri, yayin da ake fuskantar tashin hankali a yankin gabas ta tsakiya, da hauhawar farashin man fetur a wurare daban daban na duniya? To, wani babban dalilin da ya sa haka shi ne ci gaban kasar Sin a fannin sabunta nau’in makamashi.

Kasar Sin a matsayinta na kasa mafi karfin masana’antu a duniya, ta fi shigowa da danyen mai daga sauran kasashe. Kuma ta san cewa, don tabbatar da tsaro a fannin makamashi, abu mafi muhimmanci ba sayo karin mai daga mabambantan kasashe ba ne, a’a, abun yi shi ne rage dogaro kan makamashi na mai.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Saboda haka kasar Sin ta dade tana kokarin raya makamashi mai tsabta. Zuwa yanzu, kasar Sin tana kan gaba a duniya cikin shekaru 15 a jere, a fannin girke na’urorin samar da wutar lantarki ta karfin iska.

Kana kasar ta zama ta farko a duk fadin duniya cikin shekaru 10 a jere, ta fuskar kafa tashoshin samar da lantarki ta hasken rana.

Ya zuwa karshen shekarar 2025, kasar Sin ta riga ta kafa wani tsarin makamashi mai tsabta mafi girma a duniya a cikin gidanta, inda yawan makamashi mai tsabta da ta yi amfani da shi a cikin dukkan makamashin da ta samar ya kai kaso 21.7%.

Sai dai hade tattalin arzikin Sin da na sauran kasashe, ya sa ci gaban kasar Sin shi ma ya haifar da ci gaba a sauran kasashe. Zuwa yanzu, kasar Sin ta yi hadin gwiwa da kasashe da yankuna fiye da 100 a fannin makamashi mai tsabta, kana ta samar da fiye da kaso 80% na na’urorin samar da wutar lantarki ta hasken rana da ake amfani da su a duniya, da kaso 70% na na’urorin samar da lantarki ta karfin iska.

Ban da haka, kasar ta yi kokarin raba fasahohin raya tattalin arziki ta dabaru masu kare muhalli ga sauran kasashe, inda ta samar da horo ga mutane fiye da dubu 10 na kasashe masu tasowa fiye da 120, zuwa karshen shekarar 2025.

Dangane da rawar da kasar Sin ke takawa a fannin sabunta nau’in makamashi a duniya, wani marubuci mai suna Akin Yusuf, ya rubuta a cikin wata makalarsa da aka wallafa a jaridar Independent ta Najeriya cewa, kasar Sin abokiya ce da ake iya dogaro da ita, yayin da ake neman raya makamashi mai tsabta.

A cewarsa, “Ba kamar kasashen yamma ba, kasar Sin ba ta gindaya sharadin siyasa, kuma ba ta neman yin babakere a fannin mallakar fasahohi, yayin da take samar da fasahohi da kayayyaki masu alaka da sabon makamashi ga kasashe masu tasowa.

A ko da yaushe, kasar Sin tana tsayawa kan manufar samun daidaito da tabbatar da moriyar juna, inda ba kawai tana samar da fasahohi da kayayyaki ga sauran kasashe masu tasowa ba ne, har ma tana ba su taimako wajen horar da kwararru.” Mista Akin Yusuf ya kuma kara da cewa, bisa karfinta a fannin kimiyya da fasaha, da niyyarta ta sauke nauyin dake bisa wuyan babbar kasa, Sin ta samar da fasahohin sabunta makamashi, da raya tattalin arziki ga sauran kasashe masu tasowa. (Bello Wang)

Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Matan APC A Kaduna Sun Gargadi Masu Shirin Zanga-zanga

Matan APC A Kaduna Sun Gargadi Masu Shirin Zanga-zanga

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.