ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Hanyar Kyautata Fasahar Makamashi Kasar Sin Na Samar Da Damar Raya Kasa Ga Sauran Kasashe

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 months ago

A duniyarmu, akwai kasar da ta kan ambaci burinta na sake zama wata kasa mai karfi. Sai dai mai karfi ba ya nufin wanda za a iya ta da rikici a duniya, ko kuma cin zarafin sauran kasashe yadda ya ga dama.

Hakika karfin wata kasa yana bayyana ne kawai ta hanyar kiyaye wani yanayi na ci gaban tattalin arzikinta, gami da raba damar ci gaba tare da sauran kasashe, a lokacin da ake fama da yanayin rashin tabbas da kwanciyar hankali a duniya.

A kwanakin nan, kasar Sin ta sanar da alkaluman tattalin arzikinta a rubu’in farko na bana, wadanda suka nuna cewa, jimillar GDPn kasar ta karu da kaso 5% idan an kwatanta da jimilla ta makamancin lokacin shekarar bara, inda ta kai wani matsayi na koli bisa burin karuwar GDP da kasar ke neman samu a shekarar 2026, wato tsakanin 4.5% da 5%.

ADVERTISEMENT

Sai dai ta yaya kasar Sin ta tabbatar da karuwar tattalin arzikinta cikin sauri, yayin da ake fuskantar tashin hankali a yankin gabas ta tsakiya, da hauhawar farashin man fetur a wurare daban daban na duniya? To, wani babban dalilin da ya sa haka shi ne ci gaban kasar Sin a fannin sabunta nau’in makamashi.

Kasar Sin a matsayinta na kasa mafi karfin masana’antu a duniya, ta fi shigowa da danyen mai daga sauran kasashe. Kuma ta san cewa, don tabbatar da tsaro a fannin makamashi, abu mafi muhimmanci ba sayo karin mai daga mabambantan kasashe ba ne, a’a, abun yi shi ne rage dogaro kan makamashi na mai.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

Saboda haka kasar Sin ta dade tana kokarin raya makamashi mai tsabta. Zuwa yanzu, kasar Sin tana kan gaba a duniya cikin shekaru 15 a jere, a fannin girke na’urorin samar da wutar lantarki ta karfin iska.

Kana kasar ta zama ta farko a duk fadin duniya cikin shekaru 10 a jere, ta fuskar kafa tashoshin samar da lantarki ta hasken rana.

Ya zuwa karshen shekarar 2025, kasar Sin ta riga ta kafa wani tsarin makamashi mai tsabta mafi girma a duniya a cikin gidanta, inda yawan makamashi mai tsabta da ta yi amfani da shi a cikin dukkan makamashin da ta samar ya kai kaso 21.7%.

Sai dai hade tattalin arzikin Sin da na sauran kasashe, ya sa ci gaban kasar Sin shi ma ya haifar da ci gaba a sauran kasashe. Zuwa yanzu, kasar Sin ta yi hadin gwiwa da kasashe da yankuna fiye da 100 a fannin makamashi mai tsabta, kana ta samar da fiye da kaso 80% na na’urorin samar da wutar lantarki ta hasken rana da ake amfani da su a duniya, da kaso 70% na na’urorin samar da lantarki ta karfin iska.

Ban da haka, kasar ta yi kokarin raba fasahohin raya tattalin arziki ta dabaru masu kare muhalli ga sauran kasashe, inda ta samar da horo ga mutane fiye da dubu 10 na kasashe masu tasowa fiye da 120, zuwa karshen shekarar 2025.

Dangane da rawar da kasar Sin ke takawa a fannin sabunta nau’in makamashi a duniya, wani marubuci mai suna Akin Yusuf, ya rubuta a cikin wata makalarsa da aka wallafa a jaridar Independent ta Najeriya cewa, kasar Sin abokiya ce da ake iya dogaro da ita, yayin da ake neman raya makamashi mai tsabta.

A cewarsa, “Ba kamar kasashen yamma ba, kasar Sin ba ta gindaya sharadin siyasa, kuma ba ta neman yin babakere a fannin mallakar fasahohi, yayin da take samar da fasahohi da kayayyaki masu alaka da sabon makamashi ga kasashe masu tasowa.

A ko da yaushe, kasar Sin tana tsayawa kan manufar samun daidaito da tabbatar da moriyar juna, inda ba kawai tana samar da fasahohi da kayayyaki ga sauran kasashe masu tasowa ba ne, har ma tana ba su taimako wajen horar da kwararru.” Mista Akin Yusuf ya kuma kara da cewa, bisa karfinta a fannin kimiyya da fasaha, da niyyarta ta sauke nauyin dake bisa wuyan babbar kasa, Sin ta samar da fasahohin sabunta makamashi, da raya tattalin arziki ga sauran kasashe masu tasowa. (Bello Wang)

Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

MASU ALAKA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata
Ra'ayi Riga

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

June 17, 2026
Next Post
Matan APC A Kaduna Sun Gargadi Masu Shirin Zanga-zanga

Matan APC A Kaduna Sun Gargadi Masu Shirin Zanga-zanga

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.