ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Hanyar Kyautata Fasahar Makamashi Kasar Sin Na Samar Da Damar Raya Kasa Ga Sauran Kasashe

by Sulaiman and CGTN Hausa
3 months ago

A duniyarmu, akwai kasar da ta kan ambaci burinta na sake zama wata kasa mai karfi. Sai dai mai karfi ba ya nufin wanda za a iya ta da rikici a duniya, ko kuma cin zarafin sauran kasashe yadda ya ga dama.

Hakika karfin wata kasa yana bayyana ne kawai ta hanyar kiyaye wani yanayi na ci gaban tattalin arzikinta, gami da raba damar ci gaba tare da sauran kasashe, a lokacin da ake fama da yanayin rashin tabbas da kwanciyar hankali a duniya.

A kwanakin nan, kasar Sin ta sanar da alkaluman tattalin arzikinta a rubu’in farko na bana, wadanda suka nuna cewa, jimillar GDPn kasar ta karu da kaso 5% idan an kwatanta da jimilla ta makamancin lokacin shekarar bara, inda ta kai wani matsayi na koli bisa burin karuwar GDP da kasar ke neman samu a shekarar 2026, wato tsakanin 4.5% da 5%.

ADVERTISEMENT

Sai dai ta yaya kasar Sin ta tabbatar da karuwar tattalin arzikinta cikin sauri, yayin da ake fuskantar tashin hankali a yankin gabas ta tsakiya, da hauhawar farashin man fetur a wurare daban daban na duniya? To, wani babban dalilin da ya sa haka shi ne ci gaban kasar Sin a fannin sabunta nau’in makamashi.

Kasar Sin a matsayinta na kasa mafi karfin masana’antu a duniya, ta fi shigowa da danyen mai daga sauran kasashe. Kuma ta san cewa, don tabbatar da tsaro a fannin makamashi, abu mafi muhimmanci ba sayo karin mai daga mabambantan kasashe ba ne, a’a, abun yi shi ne rage dogaro kan makamashi na mai.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Saboda haka kasar Sin ta dade tana kokarin raya makamashi mai tsabta. Zuwa yanzu, kasar Sin tana kan gaba a duniya cikin shekaru 15 a jere, a fannin girke na’urorin samar da wutar lantarki ta karfin iska.

Kana kasar ta zama ta farko a duk fadin duniya cikin shekaru 10 a jere, ta fuskar kafa tashoshin samar da lantarki ta hasken rana.

Ya zuwa karshen shekarar 2025, kasar Sin ta riga ta kafa wani tsarin makamashi mai tsabta mafi girma a duniya a cikin gidanta, inda yawan makamashi mai tsabta da ta yi amfani da shi a cikin dukkan makamashin da ta samar ya kai kaso 21.7%.

Sai dai hade tattalin arzikin Sin da na sauran kasashe, ya sa ci gaban kasar Sin shi ma ya haifar da ci gaba a sauran kasashe. Zuwa yanzu, kasar Sin ta yi hadin gwiwa da kasashe da yankuna fiye da 100 a fannin makamashi mai tsabta, kana ta samar da fiye da kaso 80% na na’urorin samar da wutar lantarki ta hasken rana da ake amfani da su a duniya, da kaso 70% na na’urorin samar da lantarki ta karfin iska.

Ban da haka, kasar ta yi kokarin raba fasahohin raya tattalin arziki ta dabaru masu kare muhalli ga sauran kasashe, inda ta samar da horo ga mutane fiye da dubu 10 na kasashe masu tasowa fiye da 120, zuwa karshen shekarar 2025.

Dangane da rawar da kasar Sin ke takawa a fannin sabunta nau’in makamashi a duniya, wani marubuci mai suna Akin Yusuf, ya rubuta a cikin wata makalarsa da aka wallafa a jaridar Independent ta Najeriya cewa, kasar Sin abokiya ce da ake iya dogaro da ita, yayin da ake neman raya makamashi mai tsabta.

A cewarsa, “Ba kamar kasashen yamma ba, kasar Sin ba ta gindaya sharadin siyasa, kuma ba ta neman yin babakere a fannin mallakar fasahohi, yayin da take samar da fasahohi da kayayyaki masu alaka da sabon makamashi ga kasashe masu tasowa.

A ko da yaushe, kasar Sin tana tsayawa kan manufar samun daidaito da tabbatar da moriyar juna, inda ba kawai tana samar da fasahohi da kayayyaki ga sauran kasashe masu tasowa ba ne, har ma tana ba su taimako wajen horar da kwararru.” Mista Akin Yusuf ya kuma kara da cewa, bisa karfinta a fannin kimiyya da fasaha, da niyyarta ta sauke nauyin dake bisa wuyan babbar kasa, Sin ta samar da fasahohin sabunta makamashi, da raya tattalin arziki ga sauran kasashe masu tasowa. (Bello Wang)

Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas
  • Sulaiman
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Matan APC A Kaduna Sun Gargadi Masu Shirin Zanga-zanga

Matan APC A Kaduna Sun Gargadi Masu Shirin Zanga-zanga

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.