Kungiyar wayar da kan matan jam’iyyar APC ta shiyyar Kaduna ta Tsakiya dake jihar Kaduna wato (Kaduna Central APC Women Mobilization Forum), ta bayyana cikakken goyon bayanta ga duk wani mataki da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, zai dauka dangane da tsayar da ‘yan takara a shiyyar gabanin babban zaben shekarar 2027.
Kungiyar ta bayyana wannan matsaya ne yayin wani taro da ta gudanar a dakin taro na otel din Hamdala da ke birnin Kaduna, inda ta jaddada cewa hadin kai da biyayya ga shugabancin jam’iyya su ne ginshikin samun nasara a kowane zabe.
Jagorar kungiyar Madam Vera Oladotun, ta ce tana da yakinin cewa matakan da gwamnan zai dauka za su taimaka wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar APC daga sama har kasa a zaben 2027.
Har ila yau, kungiyar ta nesanta kanta daga duk wata zanga-zanga da wasu mata ke shirin gudanarwa a jihar Kaduna, inda aka danganta zanga-zangar da goyon bayan wani dan takara.
Kungiyar ta bayyana irin wadannan yunkuri a matsayin abubuwan da ka iya haddasa rikici da rarrabuwar kai a cikin jam’iyyar.
Madam Vera Oladotun, ta bayyana cewa kungiyar ba za ta shiga ko goyon bayan kowace irin zanga-zanga ba da sunan nuna rashin amincewa da wani dan takara.“Mu a matsayinmu na mata masu kishin jam’iyya, mun yanke shawarar nisanta kanmu daga duk wani abu da zai kawo rarrabuwar kai.
Muna kira ga daukacin matan APC da su ci gaba da mara wa gwamnatin Sanata Uba Sani baya domin ci gaban jihar da kuma tabbatar da nasarar jam’iyyar a zabe mai zuwa,” in ji ta.
Madam Oladotun ta kuma bayyana cewa idan har akwai wani dan takara da kungiyar za ta goyawa baya a matakin majalisar dattawa, to sun fi karkata ga Sanata Shehu Sani, wanda ta ce yana da kwarewa da gogewar wakiltar al’umma.
A cewarta, “Sanata Shehu Sani yana nuna kwarewa da jajircewa wajen kare muradun al’umma, kuma muna ganin ya cancanci sake wakiltar mu a majalisar dattawa.
”Kungiyar ta kuma yi kira ga sauran bangarorin jam’iyyar APC da su guji duk wani abu da zai kawo rabuwar kai, tare da jaddada muhimmancin hadin kai domin fuskantar kalubalen siyasa da ke tafe.
Mahalarta taron sun hada da shugabannin mata daga kananan hukumomi daban-daban na shiyyar Kaduna ta tsakiya, wadanda suka bayyana aniyarsu ta ci gaba da wayar da kan mata a kan muhimmancin shiga harkokin siyasa da kuma zabe.
A karshe, kungiyar ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da gudanar da shirye-shiryen fadakarwa da gangamin wayar da kai domin karfafa gwiwar mata su taka rawar gani wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar APC a dukkan matakai a zaben shekarar 2027.















Discussion about this post