ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matan APC A Kaduna Sun Gargadi Masu Shirin Zanga-zanga

by Shehu Yahaya and Sulaiman
2 months ago

Kungiyar wayar da kan matan jam’iyyar APC ta shiyyar Kaduna ta Tsakiya dake jihar Kaduna wato (Kaduna Central APC Women Mobilization Forum), ta bayyana cikakken goyon bayanta ga duk wani mataki da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, zai dauka dangane da tsayar da ‘yan takara a shiyyar gabanin babban zaben shekarar 2027.

Kungiyar ta bayyana wannan matsaya ne yayin wani taro da ta gudanar a dakin taro na otel din Hamdala da ke birnin Kaduna, inda ta jaddada cewa hadin kai da biyayya ga shugabancin jam’iyya su ne ginshikin samun nasara a kowane zabe.

Jagorar kungiyar Madam Vera Oladotun, ta ce tana da yakinin cewa matakan da gwamnan zai dauka za su taimaka wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar APC daga sama har kasa a zaben 2027.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, kungiyar ta nesanta kanta daga duk wata zanga-zanga da wasu mata ke shirin gudanarwa a jihar Kaduna, inda aka danganta zanga-zangar da goyon bayan wani dan takara.

Kungiyar ta bayyana irin wadannan yunkuri a matsayin abubuwan da ka iya haddasa rikici da rarrabuwar kai a cikin jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Madam Vera Oladotun, ta bayyana cewa kungiyar ba za ta shiga ko goyon bayan kowace irin zanga-zanga ba da sunan nuna rashin amincewa da wani dan takara.“Mu a matsayinmu na mata masu kishin jam’iyya, mun yanke shawarar nisanta kanmu daga duk wani abu da zai kawo rarrabuwar kai.

Muna kira ga daukacin matan APC da su ci gaba da mara wa gwamnatin Sanata Uba Sani baya domin ci gaban jihar da kuma tabbatar da nasarar jam’iyyar a zabe mai zuwa,” in ji ta.

Madam Oladotun ta kuma bayyana cewa idan har akwai wani dan takara da kungiyar za ta goyawa baya a matakin majalisar dattawa, to sun fi karkata ga Sanata Shehu Sani, wanda ta ce yana da kwarewa da gogewar wakiltar al’umma.

A cewarta, “Sanata Shehu Sani yana nuna kwarewa da jajircewa wajen kare muradun al’umma, kuma muna ganin ya cancanci sake wakiltar mu a majalisar dattawa.

”Kungiyar ta kuma yi kira ga sauran bangarorin jam’iyyar APC da su guji duk wani abu da zai kawo rabuwar kai, tare da jaddada muhimmancin hadin kai domin fuskantar kalubalen siyasa da ke tafe.

Mahalarta taron sun hada da shugabannin mata daga kananan hukumomi daban-daban na shiyyar Kaduna ta tsakiya, wadanda suka bayyana aniyarsu ta ci gaba da wayar da kan mata a kan muhimmancin shiga harkokin siyasa da kuma zabe.

A karshe, kungiyar ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da gudanar da shirye-shiryen fadakarwa da gangamin wayar da kai domin karfafa gwiwar mata su taka rawar gani wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar APC a dukkan matakai a zaben shekarar 2027.

Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Bayan Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Zailani, Rikicin APC Ya Ƙara Zafi A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ya Dace ‘Yan Arewa Su Ƙara Marawa Tinubu Baya Domin Kammala Wa’adi Na Biyu — Shehu Sani
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Zargin Ware Ɓangaren El-rufa’i: Rikicin Cikin Gida Ya Kaure A Jam’iyyar ADC, Kaduna
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Sin Ta Bai Wa Iran Agajin Gaggawa Na Jin Kai

Sin Ta Bai Wa Iran Agajin Gaggawa Na Jin Kai

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.