ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matan APC A Kaduna Sun Gargadi Masu Shirin Zanga-zanga

by Shehu Yahaya and Sulaiman
3 months ago

Kungiyar wayar da kan matan jam’iyyar APC ta shiyyar Kaduna ta Tsakiya dake jihar Kaduna wato (Kaduna Central APC Women Mobilization Forum), ta bayyana cikakken goyon bayanta ga duk wani mataki da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, zai dauka dangane da tsayar da ‘yan takara a shiyyar gabanin babban zaben shekarar 2027.

Kungiyar ta bayyana wannan matsaya ne yayin wani taro da ta gudanar a dakin taro na otel din Hamdala da ke birnin Kaduna, inda ta jaddada cewa hadin kai da biyayya ga shugabancin jam’iyya su ne ginshikin samun nasara a kowane zabe.

Jagorar kungiyar Madam Vera Oladotun, ta ce tana da yakinin cewa matakan da gwamnan zai dauka za su taimaka wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar APC daga sama har kasa a zaben 2027.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, kungiyar ta nesanta kanta daga duk wata zanga-zanga da wasu mata ke shirin gudanarwa a jihar Kaduna, inda aka danganta zanga-zangar da goyon bayan wani dan takara.

Kungiyar ta bayyana irin wadannan yunkuri a matsayin abubuwan da ka iya haddasa rikici da rarrabuwar kai a cikin jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Madam Vera Oladotun, ta bayyana cewa kungiyar ba za ta shiga ko goyon bayan kowace irin zanga-zanga ba da sunan nuna rashin amincewa da wani dan takara.“Mu a matsayinmu na mata masu kishin jam’iyya, mun yanke shawarar nisanta kanmu daga duk wani abu da zai kawo rarrabuwar kai.

Muna kira ga daukacin matan APC da su ci gaba da mara wa gwamnatin Sanata Uba Sani baya domin ci gaban jihar da kuma tabbatar da nasarar jam’iyyar a zabe mai zuwa,” in ji ta.

Madam Oladotun ta kuma bayyana cewa idan har akwai wani dan takara da kungiyar za ta goyawa baya a matakin majalisar dattawa, to sun fi karkata ga Sanata Shehu Sani, wanda ta ce yana da kwarewa da gogewar wakiltar al’umma.

A cewarta, “Sanata Shehu Sani yana nuna kwarewa da jajircewa wajen kare muradun al’umma, kuma muna ganin ya cancanci sake wakiltar mu a majalisar dattawa.

”Kungiyar ta kuma yi kira ga sauran bangarorin jam’iyyar APC da su guji duk wani abu da zai kawo rabuwar kai, tare da jaddada muhimmancin hadin kai domin fuskantar kalubalen siyasa da ke tafe.

Mahalarta taron sun hada da shugabannin mata daga kananan hukumomi daban-daban na shiyyar Kaduna ta tsakiya, wadanda suka bayyana aniyarsu ta ci gaba da wayar da kan mata a kan muhimmancin shiga harkokin siyasa da kuma zabe.

A karshe, kungiyar ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da gudanar da shirye-shiryen fadakarwa da gangamin wayar da kai domin karfafa gwiwar mata su taka rawar gani wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar APC a dukkan matakai a zaben shekarar 2027.

Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
  • Sulaiman
    Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas
  • Sulaiman
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
Siyasa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Next Post
Sin Ta Bai Wa Iran Agajin Gaggawa Na Jin Kai

Sin Ta Bai Wa Iran Agajin Gaggawa Na Jin Kai

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.