ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron APC A Zamfara: Ƙarfin Gwamnati Na Rataye Ne Da Kyawawan Tsare-tsaren Jam’iyya – Gwamna Lawal

by Sulaiman
1 month ago
APC

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jaddada cewa nasara da ɗorewar kowace gwamnati na da alaƙa kai tsaye da ƙarfinta a fagen siyasa, musamman yadda jam’iyyarta ke da tsari mai ƙarfi da haɗin kai.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin da ya halarci taron zaɓen shugabannin jam’iyyar APC na Jihar Zamfara, wanda aka gudanar a filin baje kolin kasuwanci da ke Gusau.

A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, wakilai 745 daga ƙananan hukumomi 14 da kuma mazabu 147 na jihar ne suka zaɓi sabbin shugabannin jam’iyyar APC ta jihar ta hanyar amincewa da juna ba tare da gardama ba.

ADVERTISEMENT
APC

Sanarwar ta ƙara da cewa, Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, Hadiza Sabuwa Balarabe, wadda ta jagoranci kwamitin gudanar da zaɓen, ita ce ta tabbatar da sakamakon tare da halartar rantsar da sabbin shugabannin jam’iyyar.

A jawabin da ya gabatar, Gwamna Lawal ya bayyana taron a matsayin lokaci mai muhimmanci kuma mai ma’ana ga ci gaban jam’iyyar, yana mai cewa hakan wata dama ce ta ƙarfafa tsarin jam’iyya da inganta dimokuraɗiyya a cikinta.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Ya ce, “Wannan tsari da ya kai ga zaɓe, tabbatarwa da kuma rantsar da sabbin shugabanni, wani muhimmin mataki ne da ke ƙara tabbatar da gaskiya, adalci da sahihancin jam’iyyarmu a matakin jiha da ƙasa.”

Gwamnan ya kuma gode wa shugabannin jam’iyyar a matakin ƙasa bisa jagoranci da goyon bayan da suke bayarwa wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya a cikin APC, tare da yabawa kwamitin zaɓen bisa ƙwarewa da gaskiyar da suka nuna wajen gudanar da aikin.

Ya ƙara da cewa, taron ya kasance wata hanya ce ta sabunta alƙawarin jam’iyyar na haɗin kai, ladabi, haɗa kowa da kowa da kuma yi wa jama’a hidima, yana mai jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da aiwatar da tsare-tsare da suka shafi tsaro, noma, ilimi, lafiya, gine-gine da bunƙasar tattalin arziki domin tabbatar da ci gaba mai ɗorewa a Zamfara.

“Mun san cewa ƙarfan gwamnati yana fitowa ne daga ƙarfan ginshiƙin siyasa. Jam’iyya mai haɗin kai da tsari mai kyau ita ce ke samar da ingantaccen shugabanci da ci gaba. Wannan taro na da matuƙar muhimmanci wajen daidaita tsarin jam’iyya da manufofin gwamnati,” in ji shi.

APC

A nasa jawabin karɓar muƙami, sabon Shugaban APC na Jihar Zamfara, Honorabul Kabiru Moyi B/Magaji, ya yi alƙawarin inganta dimokuraɗiyya a cikin jam’iyyar tare da ƙarfafa haɗin kai a tsakanin mambobinta.

APC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
peter

Rikicin Siyasa: Peter Obi Ya Fice Daga ADC

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.