ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron APC A Zamfara: Ƙarfin Gwamnati Na Rataye Ne Da Kyawawan Tsare-tsaren Jam’iyya – Gwamna Lawal

by Sulaiman
4 months ago
APC

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jaddada cewa nasara da ɗorewar kowace gwamnati na da alaƙa kai tsaye da ƙarfinta a fagen siyasa, musamman yadda jam’iyyarta ke da tsari mai ƙarfi da haɗin kai.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin da ya halarci taron zaɓen shugabannin jam’iyyar APC na Jihar Zamfara, wanda aka gudanar a filin baje kolin kasuwanci da ke Gusau.

A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, wakilai 745 daga ƙananan hukumomi 14 da kuma mazabu 147 na jihar ne suka zaɓi sabbin shugabannin jam’iyyar APC ta jihar ta hanyar amincewa da juna ba tare da gardama ba.

ADVERTISEMENT
APC

Sanarwar ta ƙara da cewa, Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, Hadiza Sabuwa Balarabe, wadda ta jagoranci kwamitin gudanar da zaɓen, ita ce ta tabbatar da sakamakon tare da halartar rantsar da sabbin shugabannin jam’iyyar.

A jawabin da ya gabatar, Gwamna Lawal ya bayyana taron a matsayin lokaci mai muhimmanci kuma mai ma’ana ga ci gaban jam’iyyar, yana mai cewa hakan wata dama ce ta ƙarfafa tsarin jam’iyya da inganta dimokuraɗiyya a cikinta.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

Ya ce, “Wannan tsari da ya kai ga zaɓe, tabbatarwa da kuma rantsar da sabbin shugabanni, wani muhimmin mataki ne da ke ƙara tabbatar da gaskiya, adalci da sahihancin jam’iyyarmu a matakin jiha da ƙasa.”

Gwamnan ya kuma gode wa shugabannin jam’iyyar a matakin ƙasa bisa jagoranci da goyon bayan da suke bayarwa wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya a cikin APC, tare da yabawa kwamitin zaɓen bisa ƙwarewa da gaskiyar da suka nuna wajen gudanar da aikin.

Ya ƙara da cewa, taron ya kasance wata hanya ce ta sabunta alƙawarin jam’iyyar na haɗin kai, ladabi, haɗa kowa da kowa da kuma yi wa jama’a hidima, yana mai jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da aiwatar da tsare-tsare da suka shafi tsaro, noma, ilimi, lafiya, gine-gine da bunƙasar tattalin arziki domin tabbatar da ci gaba mai ɗorewa a Zamfara.

“Mun san cewa ƙarfan gwamnati yana fitowa ne daga ƙarfan ginshiƙin siyasa. Jam’iyya mai haɗin kai da tsari mai kyau ita ce ke samar da ingantaccen shugabanci da ci gaba. Wannan taro na da matuƙar muhimmanci wajen daidaita tsarin jam’iyya da manufofin gwamnati,” in ji shi.

APC

A nasa jawabin karɓar muƙami, sabon Shugaban APC na Jihar Zamfara, Honorabul Kabiru Moyi B/Magaji, ya yi alƙawarin inganta dimokuraɗiyya a cikin jam’iyyar tare da ƙarfafa haɗin kai a tsakanin mambobinta.

APC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje
  • Sulaiman
    Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna
Siyasa

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Next Post
peter

Rikicin Siyasa: Peter Obi Ya Fice Daga ADC

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.