• Leadership Hausa
Monday, October 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tasirin Karancin Kudade Ga Kananan Sana’o’i

by Hussaini Najidda Umar
8 months ago
in Rahotonni
0
Tasirin Karancin Kudade Ga Kananan Sana’o’i
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shin wannan matsala da ‘yan Nijeriya suka shiga ta hada-hadar kudade tana shafar kananan sana’oi ko kawai masu mnayan kudade ne suke shan wahala? A ‘yan kwanakin nan babu abin da ludayinsa ke kan dawo irin tsarin sauya launin kudade a Nijeriya.

Kamar yadda kowa ya sani ne babban bankin Nijeriya wato CBN ya sauya launin takardun kudi wato takardar Naira 1000 da Naira 500 da 200. Kafin zuwa karshen watan Janairu duk ‘yan Nijeriya masu wadancan kudade sun garzaya bankuna don kai tsoffin kudade don musanyasu da sababbi.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Dakatar Da CBN Da Buhari Ƙara Wa’adin Maye Tsoffin Kuɗi

Kowa na sane da yadda mutane suka shiga halin dimuwa da wahala wajen sauya takardun kudaden nasu. Sannan kuma yadda jama’ar Nijeriya suka dimauce ta neman kudade a hannu shima wani hali ne da ‘yan Nijeriya suka tsinci kansu inda takardun kudi musamman sababbin suka zama kamar wasu gwalagwalai.

A ranar Lahadin karshen watan Janairun wannan shekarar Shugaba Muhammadu Buhari ya kara wa ‘yan Nijeriya kwanaki goma don su ci gaba da sauran tsoffin kudaden da suke rage a hannunsu. Saboda kiraye kiraye da shugabanni suka yin a neman an janye shirin zuwa wani lokaci.

Majalisar dokokin kasa ta dattijai da ta wakilai suma sunyin nasun kokarin wajen jawo hankalin babban bankin Nijeriya don ya sauya tunani, wajen sauya launin kudin. A haka ne ita majalisar wakilai ta yi wani kudiri inda ta nemi tsarin sauya fasalin kudin ya kai watan Yulin wannan shekarar don bai wa ‘yan Nijeriya damar canja kudadensu don gudun asara.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Gudanar Da Maulidin Manzon Allah (SAW) Na Bana

Bukukuwan Maulidin Bana: Malamai Da Shugabanni Sun Yi Kiran Addu’o’i Ga Kasa

Hakika wannan tsari na babban bankin Nijeriya ya zo wa da ‘yan Nijeriya wata sabuwar wahala wacce har yanzu take yi wa ‘yan Nijeriyar barazana na hana su yin kasuwanci cikin jin dadi da annashuwa.

Kowa na tare da sanin cewa bankunan kasuwanci na Nijeriya sun taka muhimmiyar gudunmawa wajen kuma ta’azzara wannan wahala ga ‘yan Nijeriya.

Har ila yau wannan tsarin na babban bankin Nijeriya kamar yadda wasu masana tattalin arziki suka fada sun ce ba zai yi wa masu kananan sana’oi dadi ba musamman wadanda suka dogara kacokan wajen hulda da kudade a fili. Misali kowa ya sani cewa ‘yan kasuwa da suke sayar da abubuwan amfanin yau da kullum kamar kayan abinci da sauran kananan abubuwa wadanda sai dasu mutane suke samu suyi amfani da su don cin abinci. Kamar kayan miya da man girki da ake auna wa kadan-kadan akan karamin farashi da suaransu.

Irin wadannan sana’oi hakika da yawan ‘yan Nijeriya wadannan sana’o’in da su suka dogara. Saboda haka a wannan hali da ake cikin yanzu su irin wadannan kasuwanci su ne suke shan bugu saboda karancin kudade da yake hannun mutane. Sannan kuma kamar yadda na dada a baya su dai wadannan sana’oi yawanci masu yinsu ba su da asusun banki.

Ta haka ne ya sa da yawansu suke shan wahala wajen yin ta’ammali da mutane. Kamar yadda na ga wata mace a mota tazo tana sayen doya a wajen wani mai sayar da doyar bayan ta gama ciniki sai ta fadawa mai doya ya bata lamabar asusu za ta tura masa, a nan me doya ya ce ai shi sam bai san zance ba.

Haka matar nan tana ji tana gani ta hakura ta bashi doyarsa. Anan hakika wannan me doya ya yi rashin wannan ciniki saboda kawai ba shi da lambar akawunt na banki ko nace bashi da asusun banki.

Mutane da yawa ‘yan Nijeriya masu kananan sana’oi hakika suna da kalubale na mallakar asusun banki, saboda yadda su kansu bankunan ba sa samar da tsari me kyau wanda zai sa ‘yan Nijeriya su yi hulda da su. Kowa na sane da yadda yanzu shi kansa yadda aikin sabis na intanet ya ke wahalar da mutane wajen tura kudade zuwa asusun jama’a. Musanman lokacin da aka fara wannan aiki na sauya launin kudade.

Kananan sana’oi a kasashen da suka damu da ‘yan kasar suna yin tsari me kyau ta yadda duk wasu tsare tsare da aka kirkira a cikin kasa suna bawa ‘yan kasar dama ta yadda ba za su sha wahala ba ko kadan bayan samar da tsare-tsare.

A nan ya zama dole ga gwamnatocinmu su rika saka ‘yan kasa a cikin tsare-tsarensu a duk lokacin da suka fito da wani sabon tsari don saukakawa ‘yan kasar. Kananan sana’o’i a duk kasashen duniya su ne kashin bayan ci gaban tattalin arziki, duk sanda aka samu matsala wajen kula da wadannan sana’o’i to hakika jama’a da yawa za su ji jiki, kamar yadda yanzu ‘yan Nijeriya suke gani.

Sannan kuma ya zama dole muma ‘yan Nijeriya mu dawo daga tunani irin na da, domin rungumar ci gaba da duniyar fasaha take zuwa da su.

Ya zama dole ga jama’a da su bude asusun ajiya a bankuna domin taimakon kasuwancinsu da kuma bai wa kudadensu tsaro mai inganci. Har’ila yau suma bankunan dole su samar da tsaro da karfin fasaha wajen kare dukiyoyin jama’a da don rungumar wannan tsarin na takaita amfani da kudade a fili.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gakpo Ya Yi Gaggawar Koma Wa Liverpool, Cewar Koeman

Next Post

Duk Wanda Zai Yi Noma Ya Tabbatar Da Kiyaye Lokaci – AFAN

Related

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Gudanar Da Maulidin Manzon Allah (SAW) Na Bana
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Gudanar Da Maulidin Manzon Allah (SAW) Na Bana

3 days ago
Bukukuwan Maulidin Bana: Malamai Da Shugabanni Sun Yi Kiran Addu’o’i Ga Kasa
Rahotonni

Bukukuwan Maulidin Bana: Malamai Da Shugabanni Sun Yi Kiran Addu’o’i Ga Kasa

3 days ago
Biyafara
Rahotonni

Manyan Hafsoshin Sojin Nijeriya Da Suka Fafata Yakin Biyafara

1 week ago
Kanjamau
Rahotonni

Zargin Daura Aure Da Mai Kanjamau: Yadda Aka Tube Hakimi A Katsina

1 week ago
Arewa maso Gabas
Rahotonni

A Dau Darasi Daga Asarar Dala Biliyan 100 Sakamakon Rikicin Arewa Maso Gabas

1 week ago
Kotu Ta Yanke Wa Wani Tsoho Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Har Abada Kan Laifin Fyade A Jigawa
Rahotonni

Kotu Ta Daure Wata Matashiya Kan Satar Katin Waya Na ₦275,400 A Kaduna

2 weeks ago
Next Post
Duk Wanda Zai Yi Noma Ya Tabbatar Da Kiyaye Lokaci – AFAN

Duk Wanda Zai Yi Noma Ya Tabbatar Da Kiyaye Lokaci - AFAN

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Amince Da Biyan Ma’aikata Karin Albashin N35,000 Na Wucin Gadi

Tinubu Ya Amince Da Biyan Ma’aikata Karin Albashin N35,000 Na Wucin Gadi

October 2, 2023
Mata

Ilimin ‘Ya’ya Mata: Kano Ta Fara Bai Wa ‘Yan Mata 45,000 Tallafin N20, 000

October 2, 2023
Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

October 1, 2023
Tinubu

Ranar ‘Yanci: Tinubu Ya Kara Wa Kananan Ma’aikata N25,000 Kan Albashinsu

October 1, 2023
Hangzhou

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

October 1, 2023
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

October 1, 2023
BUA

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

October 1, 2023
Kasar Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

October 1, 2023
Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

October 1, 2023
Amurka

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

October 1, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.