ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Da Kwankwaso Sun Gana A Faransa

by Sadiq
3 years ago
Tinubu

Zababben shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya gana da Sanata Rabi’u Kwankwaso, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, a zaben 2023 a kasar Faransa.

Shugabannin biyu sun gana a birnin Paris a ranar Litinin, kuma rahotanni sun ce sun tattauna batutuwan da suka shafi zaben shugabannin majalisar gabanin kaddamar da babban taron kasa karo na 10 a ranar 13 ga watan Yuni.

  • Zargin Dakatar Da Makarfi A PDP Tatsuniya Ce –Shugaba
  • DSS Ta Kama ‘Yan Ta’adda 3 A Kaduna Da Kano

LEADERSHIP ta ruwaito cewa Tinubu ya bar Nijeriya ne a ranar Laraba, 10 ga watan Mayu zuwa Turai.

ADVERTISEMENT

Rahotanni sun bayyana cewa zababben shugaban kasar ya shaida wa Kwankwaso cewa ya tuntubi abokan siyasarsa kan bukatar yin aiki tare.

An ce shugaban mai jiran gado da bakon nasa sun amince da gudanar da taruka na gaba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Yayin da uwargidan Kwankwaso da Abdulmimin Jibrin Kofa, zababben dan majalisar wakilai na NNPP, suka raka shi wurin taron, uwargidan Tinubu da Femi Gbajabiamila, kakakin majalisar wakilai mai barin gado, na daga cikin wadanda suka halarci taron.

“Zababben shugaban kasa da Sanata Kwankwaso sun yi ganawar sama da sa’o’i hudu a birnin Paris ranar Litinin. Taron wanda aka fara da misalin karfe 12:30 na rana ya kare da misalin karfe 4:45 na yamma. Taron ya samu halartar shugaban majalisar wakilai Hon Femi Gbajabiamila.

Zababben dan majalisar wakilai daga Kano, Hon Abdulmumin Jibrin ne ya raka Kwankwaso,” in ji rahoton.

“Sanata Oluremi Tinubu ita ma ta je wajen taron, inda ta tarbi matar Kwankwaso, Hajiya Salamatu, wacce ta zo da mijinta. Tattaunawar ta ta’allaka ne kan doguwar abota da suka yi tun zamanin da suka yi a Majalisar Dokoki ta kasa a shekarar 1992, hadin kan kasa da ci gaban kasa, abubuwan da suka sa a gaba ga sabuwar gwamnati, fafatawar ‘yan majalisun kasa da kuma shirin da zababben shugaban kasa ya yi na kafa gwamnatin hadin kan kasa da Kwankwaso ya yi a baya.”

Majiyar ta ce Tinubu ya kuma yi tsokaci kan sasanta Gwamna Abdullahi Ganduje da Sanata Kwankwaso.

Ganduje ya gaji Kwankwso ne a 2015, amma ‘yan siyasar biyu sun yi hannun riga da juna.

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Zai Bunkasa Ayyukan Masana’antu A Afrika

Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Zai Bunkasa Ayyukan Masana’antu A Afrika

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.