Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ƙaddamar da gadar ƙasa mai tsawon mita 600 da hanyoyin cikin gari masu tsawon kilomita 3.7 da aka faɗaɗa a Akwanga, waɗanda gwamnatin Abdullahi Sule ta gina a matsayin wani ɓangare na shirin sabunta birane.
Shugaban ƙasar, wanda Nentawe Yilwatda ya wakilta, ya ce aikin zai rage cunkoson ababen hawa tare da bunƙasa tattalin arziki, yana mai yabawa gwamnatin jihar kan ayyukan ci gaba da take aiwatarwa.
A nasa jawabin, Gwamna Abdullahi Sule ya ce gwamnatin jihar ta gudanar da ayyukan ne ba tare da karɓar rance daga banki ba, sakamakon ƙarin kuɗaɗen shiga da suka biyo bayan sauye-sauyen tattalin arzikin gwamnatin tarayya.
Ya kuma bayyana cewa al’ummar Jihar Nasarawa za su ci gaba da mara wa Shugaba Tinubu baya a zaɓen shekarar 2027 saboda ayyukan ci gaban da gwamnatin sa ke aiwatarwa.














