Gwamnatin Jihar Nasarawa ta tanadi isassun jami’an tsaro domin tabbatar da gudanar da zaɓen fidda gwani na Jam’iyyar APC cikin lumana da kwanciyar hankali, wanda zai fara ranar Juma’a, 15 ga Mayu, 2026.
Da yake zantawa da manema labarai, Mai Taimaka wa Gwamna Abdullahi Sule kan harkokin hulɗa da al’umma, Kwamared Piter Ahmba, ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta ɗauki wannan mataki ne domin tabbatar da sahihin zaɓe cikin kwanciyar hankali.
Ya ce babu wani ɗan takara da gwamnatin jihar ta tilasta masa janyewa domin goyon bayan wani ɗan takara.
A cewarsa, dukkan ‘yan takarar sun cancanta, kuma kowannensu na da muhimmiyar rawa da zai taka idan aka tsayar da shi takara.
Kwamared Piter Ahmba ya ƙara da cewa za a gudanar da zaɓen kai tsaye ba tare da maguɗi ba, tare da bin dokokin zaɓe yadda ya kamata.
Ya bayyana cewa za a yi amfani ne kawai da sahihin katin jam’iyya mai cikakken bayani da shaidar tantancewa.
Haka kuma, ya yaba wa ‘yan takarar APC bisa yadda suke gudanar da harkokin siyasa cikin tsafta, fahimtar juna da zaman lafiya a jihar.
Ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta sha alwashin bayyana duk wanda ya yi nasara a zaɓen cikin gaskiya da adalci.
A ƙarshe, ya yi kira ga ‘yan jarida da su kasance masu bayar da sahihan rahotanni game da yadda zaɓen ya gudana ba tare da nuna son kai ko wariya ba.
Ya ce al’ummar jihar da ba za su samu damar halartar wajen zaɓen ba za su dogara ne da kafafen yaɗa labarai domin samun bayanai, don haka ya kamata a riƙa faɗin gaskiya ga jama’a.















Discussion about this post