Gwamnatin Jihar Nasarawa ta rufe kamfanin haƙar ma’adanai na Lideal Mines Company da ke aiki a yankin ci gaban raya Kasa dake Udege, a ƙaramar hukumar Nasarawa, sakamakon wani rikicin shari’a da ya daɗe yana gudana tsakanin gwamnatin jihar da kamfanin.
Kwamishinar Muhalli da Albarkatun Ƙasa ta Jihar Nasarawa, Dakta Margaret Elayo, ce ta bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a Lafia, babban birnin jihar.
Dakta Elayo ta bayyana cewa bayan jerin tattaunawa da masu ruwa da tsaki tare da nazarin rahotannin tsaro da suka shafi ayyukan haƙar ma’adanai a yankunan da abin ya shafa, gwamnatin jihar ta umarci kamfanin da ya fara janye dukkan kayayyakin aikinsa daga wurin nan take.
A cewarta, umarnin ya haɗa da cire injinan haƙar ma’adanai, manyan motoci, sauran kayan aiki da kuma ma’aikatan kamfanin daga wurin haƙar ma’adanan.
Ta ce matakin ya yi daidai da ƙudirin Gwamna Abdullahi Sule na tabbatar da halastattun ayyukan haƙar ma’adanai, kiyaye zaman lafiya a yankunan ma’adinai da kuma tabbatar da bin umarnin gwamnati da ƙa’idojin aiki da aka gindaya a jihar.
Kwamishinar ta ƙara da cewa gwamnatin jihar ta bai wa kamfanin wa’adin da zai cika domin bin umarnin gaba ɗaya.
Ta ce:“Umarnin ya kuma tanadi dakatar da duk wani nau’i na ayyukan haƙar ma’adanai da kuma fitar da albarkatun ƙasa daga wurin cikin wa’adin da aka bayar.“
Gwamnati ta bayyana a sarari cewa an ɗauki wannan mataki ne domin kare muradun jama’a da kuma ci gaba da ƙoƙarin sake tsara fannin haƙar ma’adanai a Jihar Nasarawa ta yadda za a samu saka hannun jari mai inganci, ƙara darajar albarkatun ƙasa a cikin gida, da haɗin kan al’umma da ci gaban tattalin arziki mai ɗorewa.
“Gwamnan ya sha nanata cewa duk ayyukan haƙar ma’adanai a jihar dole ne su dace da manufofin gwamnati, musamman buƙatar masu saka hannun jari su kafa ingantattun cibiyoyin sarrafa ma’adanai da za su amfani al’ummomin da ke yankunan da ake haƙar ma’adanan tare da bayar da gudunmawa mai ma’ana ga tattalin arzikin jihar.”
Dakta Elayo ta ƙara da cewa gwamnatin jihar za ta tura jami’an tsaro zuwa wurin haƙar ma’adanan domin tabbatar da cikakken bin umarnin da aka bayar.
Ta kuma jaddada cewa gwamnatin Jihar Nasarawa na ci gaba da jajircewa wajen samar da yanayi mai kyau ga sahihan masu saka hannun jari da ke shirye su bi dokoki, manufofi da muradun ci gaban jihar.















Discussion about this post