ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Nasarawa Ta Rufe Kamfanin Haƙar Ma’adanai Saboda Rikicin Shari’a

by Zubairu M Lawal and Sulaiman
2 months ago
Nasarawa

Gwamnatin Jihar Nasarawa ta rufe kamfanin haƙar ma’adanai na Lideal Mines Company da ke aiki a yankin ci gaban raya Kasa dake Udege, a ƙaramar hukumar Nasarawa, sakamakon wani rikicin shari’a da ya daɗe yana gudana tsakanin gwamnatin jihar da kamfanin.

Kwamishinar Muhalli da Albarkatun Ƙasa ta Jihar Nasarawa, Dakta Margaret Elayo, ce ta bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a Lafia, babban birnin jihar.

Dakta Elayo ta bayyana cewa bayan jerin tattaunawa da masu ruwa da tsaki tare da nazarin rahotannin tsaro da suka shafi ayyukan haƙar ma’adanai a yankunan da abin ya shafa, gwamnatin jihar ta umarci kamfanin da ya fara janye dukkan kayayyakin aikinsa daga wurin nan take.

ADVERTISEMENT

A cewarta, umarnin ya haɗa da cire injinan haƙar ma’adanai, manyan motoci, sauran kayan aiki da kuma ma’aikatan kamfanin daga wurin haƙar ma’adanan.

Ta ce matakin ya yi daidai da ƙudirin Gwamna Abdullahi Sule na tabbatar da halastattun ayyukan haƙar ma’adanai, kiyaye zaman lafiya a yankunan ma’adinai da kuma tabbatar da bin umarnin gwamnati da ƙa’idojin aiki da aka gindaya a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Kwamishinar ta ƙara da cewa gwamnatin jihar ta bai wa kamfanin wa’adin da zai cika domin bin umarnin gaba ɗaya.

Ta ce:“Umarnin ya kuma tanadi dakatar da duk wani nau’i na ayyukan haƙar ma’adanai da kuma fitar da albarkatun ƙasa daga wurin cikin wa’adin da aka bayar.“

Gwamnati ta bayyana a sarari cewa an ɗauki wannan mataki ne domin kare muradun jama’a da kuma ci gaba da ƙoƙarin sake tsara fannin haƙar ma’adanai a Jihar Nasarawa ta yadda za a samu saka hannun jari mai inganci, ƙara darajar albarkatun ƙasa a cikin gida, da haɗin kan al’umma da ci gaban tattalin arziki mai ɗorewa.

“Gwamnan ya sha nanata cewa duk ayyukan haƙar ma’adanai a jihar dole ne su dace da manufofin gwamnati, musamman buƙatar masu saka hannun jari su kafa ingantattun cibiyoyin sarrafa ma’adanai da za su amfani al’ummomin da ke yankunan da ake haƙar ma’adanan tare da bayar da gudunmawa mai ma’ana ga tattalin arzikin jihar.”

Dakta Elayo ta ƙara da cewa gwamnatin jihar za ta tura jami’an tsaro zuwa wurin haƙar ma’adanan domin tabbatar da cikakken bin umarnin da aka bayar.

Ta kuma jaddada cewa gwamnatin Jihar Nasarawa na ci gaba da jajircewa wajen samar da yanayi mai kyau ga sahihan masu saka hannun jari da ke shirye su bi dokoki, manufofi da muradun ci gaban jihar.

Nasarawa
Zubairu M Lawal
+ posts Bio
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Mutane 600 Ne Kacal Suka Ci Jarabawar Ɗaukar Malaman Firamare Daga Cikin 8,000
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Tinubu Ya Ƙaddamar Da Gadar Ƙasa Da Tituna A Akwanga
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Gwamnati Ta Jibge Jami’an Tsaro Domin Gudanar da Zaɓen Fidda Gwanin APC A Nasarawa
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    ’Yansanda Sun Tabbatar da Sace Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa
Nasarawa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma
  • Sulaiman
    Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani
  • Sulaiman
    Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana
  • Sulaiman
    Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”
Manyan Labarai

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Gana Da ‘Yan Kasuwan Amurka Da Suka Rako Shugaban Amurka

Shugaba Xi Ya Gana Da 'Yan Kasuwan Amurka Da Suka Rako Shugaban Amurka

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.