ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Nasarawa Ta Rufe Kamfanin Haƙar Ma’adanai Saboda Rikicin Shari’a

by Zubairu M Lawal and Sulaiman
3 weeks ago
Nasarawa

Gwamnatin Jihar Nasarawa ta rufe kamfanin haƙar ma’adanai na Lideal Mines Company da ke aiki a yankin ci gaban raya Kasa dake Udege, a ƙaramar hukumar Nasarawa, sakamakon wani rikicin shari’a da ya daɗe yana gudana tsakanin gwamnatin jihar da kamfanin.

Kwamishinar Muhalli da Albarkatun Ƙasa ta Jihar Nasarawa, Dakta Margaret Elayo, ce ta bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a Lafia, babban birnin jihar.

Dakta Elayo ta bayyana cewa bayan jerin tattaunawa da masu ruwa da tsaki tare da nazarin rahotannin tsaro da suka shafi ayyukan haƙar ma’adanai a yankunan da abin ya shafa, gwamnatin jihar ta umarci kamfanin da ya fara janye dukkan kayayyakin aikinsa daga wurin nan take.

ADVERTISEMENT

A cewarta, umarnin ya haɗa da cire injinan haƙar ma’adanai, manyan motoci, sauran kayan aiki da kuma ma’aikatan kamfanin daga wurin haƙar ma’adanan.

Ta ce matakin ya yi daidai da ƙudirin Gwamna Abdullahi Sule na tabbatar da halastattun ayyukan haƙar ma’adanai, kiyaye zaman lafiya a yankunan ma’adinai da kuma tabbatar da bin umarnin gwamnati da ƙa’idojin aiki da aka gindaya a jihar.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Kwamishinar ta ƙara da cewa gwamnatin jihar ta bai wa kamfanin wa’adin da zai cika domin bin umarnin gaba ɗaya.

Ta ce:“Umarnin ya kuma tanadi dakatar da duk wani nau’i na ayyukan haƙar ma’adanai da kuma fitar da albarkatun ƙasa daga wurin cikin wa’adin da aka bayar.“

Gwamnati ta bayyana a sarari cewa an ɗauki wannan mataki ne domin kare muradun jama’a da kuma ci gaba da ƙoƙarin sake tsara fannin haƙar ma’adanai a Jihar Nasarawa ta yadda za a samu saka hannun jari mai inganci, ƙara darajar albarkatun ƙasa a cikin gida, da haɗin kan al’umma da ci gaban tattalin arziki mai ɗorewa.

“Gwamnan ya sha nanata cewa duk ayyukan haƙar ma’adanai a jihar dole ne su dace da manufofin gwamnati, musamman buƙatar masu saka hannun jari su kafa ingantattun cibiyoyin sarrafa ma’adanai da za su amfani al’ummomin da ke yankunan da ake haƙar ma’adanan tare da bayar da gudunmawa mai ma’ana ga tattalin arzikin jihar.”

Dakta Elayo ta ƙara da cewa gwamnatin jihar za ta tura jami’an tsaro zuwa wurin haƙar ma’adanan domin tabbatar da cikakken bin umarnin da aka bayar.

Ta kuma jaddada cewa gwamnatin Jihar Nasarawa na ci gaba da jajircewa wajen samar da yanayi mai kyau ga sahihan masu saka hannun jari da ke shirye su bi dokoki, manufofi da muradun ci gaban jihar.

Nasarawa
Zubairu M Lawal
+ posts Bio
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    Gwamnati Ta Jibge Jami’an Tsaro Domin Gudanar da Zaɓen Fidda Gwanin APC A Nasarawa
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    ’Yansanda Sun Tabbatar da Sace Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    NAFDAC Ta Ƙona Kayayyaki Marasa Inganci Na Naira Biliyan 5 A Nasarawa
  • Zubairu M Lawal
    https://hausa.leadership.ng/author/zubairu-m-lawal/
    An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya
Nasarawa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Shugaba Xi Ya Gana Da ‘Yan Kasuwan Amurka Da Suka Rako Shugaban Amurka

Shugaba Xi Ya Gana Da 'Yan Kasuwan Amurka Da Suka Rako Shugaban Amurka

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.