Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya umarci hukumomin tsaro da su gaggauta ceto waɗanda aka yi garkuwa da su a wani sabon harin da aka kai a Jihar Neja.
Rahotanni sun ce ‘yan bindiga sun kai hari wasu masallatai huɗu yayin da ake tsaka da sallar Juma’a a garuruwan Dekara, Kpenya, Sabon-Gida da Gidan-Zana da ke Ƙaramar Hukumar Borgu.
An ce maharan sun yi awon gaba da masallata da dama zuwa cikin daji.
Shugaba Tinubu ya yi Allah-wadai da harin da kuma kisan mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, yana mai bayyana maharan a matsayin maƙiya zaman lafiya.
Tinubu ya umarci Rundunar Sojin Nijeriya, ‘Yansanda, DSS da sauran hukumomin tsaro da su haɗa kai wajen ceto dukkanin waɗanda aka yi garkuwa da su.
Ya kuma buƙaci Hafsoshin Tsaro su riƙa ba shi rahotanni kan yadda aikin ceto ke gudana.
Shugaban ya tabbatar wa iyalan waɗanda abin ya shafa da al’ummar Jihar Neja cewa Gwamnatin Tarayya za ta bayar da dukkanin tallafin da ya dace domin inganta tsaro da kuma taimaka wa waɗanda harin ya shafa.














