Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin yin gagarumin gyara a harkar ƙwallon ƙafa ta Nijeriya, bayan tawagar ƙwallon ƙasar ta kasa samun gurbin zuwa manyan gasa a matakin ƙasa da ƙasa.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Alhamis, Tinubu ya umarci Hukumar Kula da Wasanni ta Ƙasa (NSC) da ta yi aiki tare da Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Nijeriya (NFF) da sauran masu ruwa da tsaki domin inganta yadda ake tafiyar da ƙwallon ƙafa a ƙasar.
Gyaran zai mayar da hankali kan shugabanci da gudanar da ƙwallon ƙafa, wasannin cikin gida, bunƙasa ’yan wasa da kuma tabbatar da ɗaukar alhaki.
Tinubu ya ce Nijeriya na da haziƙan ’yan wasan ƙwallon ƙafa da kuma goyon bayan jama’a, amma rashin tsarin gudanarwa ya hana ƙasar samun kyakkyawan sakamako.
Ya kuma umarci hukumomin ƙwallon ƙafa su tattauna da FIFA da Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afirka (CAF) yayin gudanar da gyaran, tare da tabbatar da cewa Nijeriya na bin ƙa’idojin ƙwallon ƙafa na duniya.
Shugaban ƙasar ya yi kira ga masu ruwa da tsaki da ’yan Nijeriya da su goyi bayan wannan mataki domin gina tsarin ƙwallon ƙafa, domin samun nasara.














