Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, ya buƙaci shugabannin Ƙungiyar Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), da su yi tsayin daka wajen hana sauyin gwamnati ba bisa ƙa’ida ba, wanda ya yi gargaɗin cewa barazanar da ke ƙara bayyana a yankin na buƙatar haɗin kai da ɗaukar mataki.
Tinubu, ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi ga shugabannin ƙungiyar a taron Majalisar Shugabannin Ƙasashe ECOWAS karo na 68 inda ya ce ya zama dole a ɗauki mataki kan iyakokin ƙasashen Yammacin Afrika domin magance barazanar tsaro.
- Juyin Mulki: ECOWAS Ta Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Yammacin Afirka
- Gwamnan Kano Ya Kafa Sabuwar Rundunar Tsaron Tashoshin Mota
Tinubu ya jaddada cewa babu wata ƙasa komai girma ko ƙarfinta, da za ta iya tabbatar da dawwamammen zaman lafiya ita kaɗai yana mai cewa matsalar tsaro da inganta walwala da juriyar yankin alhaki ne da ke kan kowa kuma hakan na buƙatar haɗin kai.
A cewarsa, barazanar da ke fuskantar Yammacin Afrika daga waje sun hada da ta’addanci da masu tsatsauran ra’ayin addini da kuma sauyin gwamnati ba bisa ka’ida ba da ma rashin jituwan tsakanin ƙasa-da-ƙasa na ƙungiyoyi da rashin tsaro a fannin yanar gizo da ma tasirin sauyin yanayi da fai karancin abinci da kuma hijira ba bisa ƙa’ida ba.
Shugaban, wanda Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya wakilta a taron, ya sake jaddada matsayar Nijeriya cewa zumunci da fahimtar juna ba tare da amfani da ƙarfi ba, su ne ya kamata su tsara makomar al’ummar ECOWAS.
Ya bayyana cewa ECOWAS ba za ta iya cimma manufarta ba har sai kowace ƙasa ta mutunta ka’idojin adalci da daidaito a harkokin cikinta, yana mai gargaɗin cewa babban ƙalubalen ƙungiyar shi ne rikici daga waje ba wai na cikin gida ba.














