Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya gana da shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago da kuma gwamnoni a daren ranar Talata domin hana shirin gudanar da zanga-zanga kan matsalar rashin tsaro.
An yi taron ne gabanin zanga-zangar ƙasa baki ɗaya da Ƙungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) ta shirya.
- Yadda Ake Hayar ’Yan Jarida Domin Ƙirƙirar Labaran Ƙarya Game Da Hukumar NAHCON
- ICPC Za Ta Binciki Zargin Da Ake Yi Wa Shugaban NMDPRA
Shugaban NLC, Joe Ajaero, ya ce ƙungiyar za ta sake duba shirin zanga-zangar bayan tattaunawa da shugaban ƙasa da Ƙungiyar Gwamnoni.
Ya bayyana cewa taron na shawara ne kawai, kuma shugabannin ƙungiyar ƙwadago za su sake zama domin yanke matsaya ta gaba.
Za a sanar da sakamakon ƙarshe a ranar Laraba.
Gwamnan Jihar Imo kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jam’iyyar APC, Hope Uzodinma, ya ce ana ci gaba da tattaunawa ne cikin fahimta domin amfanin ƙasa.
A baya, NLC ta sanar da shirin gudanar da zanga-zangar lumana a faɗin ƙasar domin nuna damuwa kan ƙara taɓarɓarewar tsaro.














