ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa, Olawepo-Hashim Ya Nemi A Gaggauta Ceto ‘Yan Makarantar Da Aka Sace A Borno Da Ogbomosho

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Gbenga Olawepo-Hashim, ya yi Allah-wadai da sace ɗaliban makarantar firamare da ƙaramar sakandare ta Mussa da ke Ƙaramar Hukumar Askira-Uba a Jihar Borno, tare da hare-haren da aka kai makarantu da dama a Ƙaramar Hukumar Oriire ta Jihar Oyo da ke yankin Ogbomosho, yana mai bayyana lamarin a matsayin “mummunan hari kan makomar Nijeriya.”

Ya kuma buƙaci gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da su ɗauki matakin gaggawa da ƙarfi, yana mai cewa ceto yaran cikin gaggawa da tabbatar da lafiyarsu dole ne ya zama babban abin fifiko ga ƙasa baki ɗaya.

Makarantun da harin ya shafa a Jihar Oyo sun haɗa da Baptist Nursery and Primary School da ke Yawota, Community Grammar School da ke Esiele, da kuma L.A. Primary School da ke Esiele.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa, Olawepo-Hashim ya ce kai hari ga yara masu makaranta na nuna wani sabon salo mai haɗari na ta’addanci da kuma kai hari kai tsaye ga ilimi, zaman lafiya da makomar ƙasa.

“Makarantu bai kamata su zama wuraren tsoro ba,” in ji shi, yana mai gargaɗin cewa yawaitar hare-hare kan cibiyoyin ilimi na iya ƙara yaɗa rashin tsaro har zuwa ga tsararraki masu zuwa.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Ya miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda abin ya shafa, sannan ya sake kira ga gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da su ɗauki mataki cikin gaggawa domin ceto yaran lafiya.

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar ya ce abubuwan da suka faru sun nuna gazawar tsarin tsaron yankunan karkara na Nijeriya, inda ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya ke anfani da wuraren da gwamnati ba ta da cikakken iko, talauci da ƙarancin kasancewar gwamnati.

Da yake magana kan kashe wani kwamandan ISIS ta haɗin gwiwar jami’an Nijeriya da Amurka, Olawepo-Hashim ya yaba da nasarar soji, amma ya yi gargaɗin cewa bai kamata a dogara da irin waɗannan nasarori kaɗai ba.

“Wannan mummunan al’amari na tuna mana cewa nasarorin yaƙi kaɗai ba za su iya tabbatar da tsaron ƙasa ba,” in ji shi.

Ya yi kira da a samar da cikakken tsarin tsaron ƙasa wanda zai haɗa da ci gaba da matsin lamba ta fuskar soja, haɗin gwiwar leƙen asiri, tsaron iyakoki, faɗaɗa tsaron karkara da kuma shirye-shiryen tattalin arziki da zamantakewa.

Olawepo-Hashim ya kuma buƙaci ƙasashen duniya da su mai da hankali sosai kan tabarbarewar tsaro a Arewacin Nijeriya, yana mai cewa matsalar na da tasiri har zuwa yankunan Yammaci da Tsakiyar Afirka.

Ya soki rashin nuna damuwa mai ɗorewa daga ƙasashen duniya, musamman kan yawaitar sace yaran Afirka, yana mai gargaɗin kada duniya ta saba da irin waɗannan munanan abubuwa.

“Kada duniya ta zama mai ɗaukar irin waɗannan abubuwa a matsayin ruwan dare,” in ji shi.

Ya kuma yi gargaɗin cewa Nijeriya ba za ta iya gina makoma mai ɗorewa ba idan ana rayuwa cikin inuwa ta tsoro.

“Babu wata ƙasa da za ta bunƙasa yayin da ake farautar yaranta kuma makarantu ke cikin hari,” in ji shi.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji 7 A Harin Kwantan Ɓauna A Sakkwato

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji 7 A Harin Kwantan Ɓauna A Sakkwato

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.