ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa, Olawepo-Hashim Ya Nemi A Gaggauta Ceto ‘Yan Makarantar Da Aka Sace A Borno Da Ogbomosho

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Gbenga Olawepo-Hashim, ya yi Allah-wadai da sace ɗaliban makarantar firamare da ƙaramar sakandare ta Mussa da ke Ƙaramar Hukumar Askira-Uba a Jihar Borno, tare da hare-haren da aka kai makarantu da dama a Ƙaramar Hukumar Oriire ta Jihar Oyo da ke yankin Ogbomosho, yana mai bayyana lamarin a matsayin “mummunan hari kan makomar Nijeriya.”

Ya kuma buƙaci gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da su ɗauki matakin gaggawa da ƙarfi, yana mai cewa ceto yaran cikin gaggawa da tabbatar da lafiyarsu dole ne ya zama babban abin fifiko ga ƙasa baki ɗaya.

Makarantun da harin ya shafa a Jihar Oyo sun haɗa da Baptist Nursery and Primary School da ke Yawota, Community Grammar School da ke Esiele, da kuma L.A. Primary School da ke Esiele.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa, Olawepo-Hashim ya ce kai hari ga yara masu makaranta na nuna wani sabon salo mai haɗari na ta’addanci da kuma kai hari kai tsaye ga ilimi, zaman lafiya da makomar ƙasa.

“Makarantu bai kamata su zama wuraren tsoro ba,” in ji shi, yana mai gargaɗin cewa yawaitar hare-hare kan cibiyoyin ilimi na iya ƙara yaɗa rashin tsaro har zuwa ga tsararraki masu zuwa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Ya miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda abin ya shafa, sannan ya sake kira ga gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da su ɗauki mataki cikin gaggawa domin ceto yaran lafiya.

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar ya ce abubuwan da suka faru sun nuna gazawar tsarin tsaron yankunan karkara na Nijeriya, inda ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya ke anfani da wuraren da gwamnati ba ta da cikakken iko, talauci da ƙarancin kasancewar gwamnati.

Da yake magana kan kashe wani kwamandan ISIS ta haɗin gwiwar jami’an Nijeriya da Amurka, Olawepo-Hashim ya yaba da nasarar soji, amma ya yi gargaɗin cewa bai kamata a dogara da irin waɗannan nasarori kaɗai ba.

“Wannan mummunan al’amari na tuna mana cewa nasarorin yaƙi kaɗai ba za su iya tabbatar da tsaron ƙasa ba,” in ji shi.

Ya yi kira da a samar da cikakken tsarin tsaron ƙasa wanda zai haɗa da ci gaba da matsin lamba ta fuskar soja, haɗin gwiwar leƙen asiri, tsaron iyakoki, faɗaɗa tsaron karkara da kuma shirye-shiryen tattalin arziki da zamantakewa.

Olawepo-Hashim ya kuma buƙaci ƙasashen duniya da su mai da hankali sosai kan tabarbarewar tsaro a Arewacin Nijeriya, yana mai cewa matsalar na da tasiri har zuwa yankunan Yammaci da Tsakiyar Afirka.

Ya soki rashin nuna damuwa mai ɗorewa daga ƙasashen duniya, musamman kan yawaitar sace yaran Afirka, yana mai gargaɗin kada duniya ta saba da irin waɗannan munanan abubuwa.

“Kada duniya ta zama mai ɗaukar irin waɗannan abubuwa a matsayin ruwan dare,” in ji shi.

Ya kuma yi gargaɗin cewa Nijeriya ba za ta iya gina makoma mai ɗorewa ba idan ana rayuwa cikin inuwa ta tsoro.

“Babu wata ƙasa da za ta bunƙasa yayin da ake farautar yaranta kuma makarantu ke cikin hari,” in ji shi.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano
Labarai

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Next Post
‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji 7 A Harin Kwantan Ɓauna A Sakkwato

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji 7 A Harin Kwantan Ɓauna A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Montenegro Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.