Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Gbenga Olawepo-Hashim, ya yi Allah-wadai da sace ɗaliban makarantar firamare da ƙaramar sakandare ta Mussa da ke Ƙaramar Hukumar Askira-Uba a Jihar Borno, tare da hare-haren da aka kai makarantu da dama a Ƙaramar Hukumar Oriire ta Jihar Oyo da ke yankin Ogbomosho, yana mai bayyana lamarin a matsayin “mummunan hari kan makomar Nijeriya.”
Ya kuma buƙaci gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da su ɗauki matakin gaggawa da ƙarfi, yana mai cewa ceto yaran cikin gaggawa da tabbatar da lafiyarsu dole ne ya zama babban abin fifiko ga ƙasa baki ɗaya.
Makarantun da harin ya shafa a Jihar Oyo sun haɗa da Baptist Nursery and Primary School da ke Yawota, Community Grammar School da ke Esiele, da kuma L.A. Primary School da ke Esiele.
A cikin wata sanarwa, Olawepo-Hashim ya ce kai hari ga yara masu makaranta na nuna wani sabon salo mai haɗari na ta’addanci da kuma kai hari kai tsaye ga ilimi, zaman lafiya da makomar ƙasa.
“Makarantu bai kamata su zama wuraren tsoro ba,” in ji shi, yana mai gargaɗin cewa yawaitar hare-hare kan cibiyoyin ilimi na iya ƙara yaɗa rashin tsaro har zuwa ga tsararraki masu zuwa.
Ya miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda abin ya shafa, sannan ya sake kira ga gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da su ɗauki mataki cikin gaggawa domin ceto yaran lafiya.
Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar ya ce abubuwan da suka faru sun nuna gazawar tsarin tsaron yankunan karkara na Nijeriya, inda ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya ke anfani da wuraren da gwamnati ba ta da cikakken iko, talauci da ƙarancin kasancewar gwamnati.
Da yake magana kan kashe wani kwamandan ISIS ta haɗin gwiwar jami’an Nijeriya da Amurka, Olawepo-Hashim ya yaba da nasarar soji, amma ya yi gargaɗin cewa bai kamata a dogara da irin waɗannan nasarori kaɗai ba.
“Wannan mummunan al’amari na tuna mana cewa nasarorin yaƙi kaɗai ba za su iya tabbatar da tsaron ƙasa ba,” in ji shi.
Ya yi kira da a samar da cikakken tsarin tsaron ƙasa wanda zai haɗa da ci gaba da matsin lamba ta fuskar soja, haɗin gwiwar leƙen asiri, tsaron iyakoki, faɗaɗa tsaron karkara da kuma shirye-shiryen tattalin arziki da zamantakewa.
Olawepo-Hashim ya kuma buƙaci ƙasashen duniya da su mai da hankali sosai kan tabarbarewar tsaro a Arewacin Nijeriya, yana mai cewa matsalar na da tasiri har zuwa yankunan Yammaci da Tsakiyar Afirka.
Ya soki rashin nuna damuwa mai ɗorewa daga ƙasashen duniya, musamman kan yawaitar sace yaran Afirka, yana mai gargaɗin kada duniya ta saba da irin waɗannan munanan abubuwa.
“Kada duniya ta zama mai ɗaukar irin waɗannan abubuwa a matsayin ruwan dare,” in ji shi.
Ya kuma yi gargaɗin cewa Nijeriya ba za ta iya gina makoma mai ɗorewa ba idan ana rayuwa cikin inuwa ta tsoro.
“Babu wata ƙasa da za ta bunƙasa yayin da ake farautar yaranta kuma makarantu ke cikin hari,” in ji shi.













Discussion about this post