ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji 7 A Harin Kwantan Ɓauna A Sakkwato

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago

Wasu da ake zargin ƴan ta’addan Lakurawa ne sun kashe sojoji bakwai a wani kwanton ɓauna da suka yi a ƙauyen Runji, mai tazarar kusan kilomita 10 daga garin Illela a Ƙaramar Hukumar Illela ta Jihar Sakkwato.

Majiyoyin yankin sun ce lamarin ya faru ne a yammacin ranar Asabar da ta gabata yayin da dakarun ke dawowa daga wani samame da suka kai maɓoyar Lakurawa.

Mazauna yankin sun bayyana cewa sojojin sun kai hari sansanin ƴan ta’addan ne da motocin soja guda uku, wani farmaki da ake kyautata zaton ya jawo wa ƴan bindigar asara mai yawa.

ADVERTISEMENT

Wata majiya da ta san yadda lamarin ya faru ta ce ɗaya daga cikin motocin sojojin ta samu matsalar inji yayin da suke komawa sansaninsu da ke Illela, lamarin da ya sa wasu daga cikin sojojin suka tsaya a gefen hanya domin gyara ta.

Da alama ƴan ta’addan sun tattaru tare da bibiyar sojojin domin ɗaukar fansa kan harin da aka kai musu a sansaninsu,” in ji majiyar.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

Ta ƙara da cewa maharan sun iso yankin ne a kan babura kusan 30, inda kowane babur ke ɗauke da mayaƙa uku masu ɗauke da muggan makamai.

“Sun tarar da sojojin a wajen da ake gyaran motar, sannan aka yi musayar wuta mai tsanani na wani lokaci,” in ji majiyar.

Sai dai wani rahoto ya ce sojoji bakwai da farar hula ɗaya ne suka rasa rayukansu a harin kwanton ɓaunar.

“Bayan sojojin sun bar motar da ta lalace, suna tafiya zuwa sansaninsu tare da taimakon wani farar hula da ya san yankin sosai, sai Lakurawa suka yi musu kwanton ɓauna suka kashe sojojin bakwai da jagoransu na farar hula,” in ji majiyar.

Wani mazaunin Illela, wanda ya nemi a sakaya sunansa saboda dalilan tsaro, ya ce an fara tabbatar da mutuwar sojoji shida a wurin da lamarin ya faru, sannan daga baya aka gano gawar wani soja a cikin wani daji da ke kusa da wurin, wanda ya sa adadin ya kai bakwai.

“Mun ga gawarwaki bakwai a wurin, sannan aka sake gano wata gawar washegari,” in ji shi.

Majiyoyin tsaro ma sun tabbatar da harin, inda suka ce an kwashe gawarwakin sojojin da aka kashe zuwa Sakkwato.

Wani jami’in gwamnati a yankin ya kuma bayyana cewa wani babban jami’in soja mai muƙamin Laftanar a rundunar sojin Nijeriya na cikin waɗanda aka kashe a harin.

Kakakin rundunar ƴansandan Jihar Sakkwato, DSP Ahmad Rufa’i, da mai bai wa gwamna shawara kan harkokin tsaro, Kanal Ahmed Usman, sun ƙi yin tsokaci kan lamarin.

Sai dai wani babban jami’in soja da ya nemi a sakaya sunansa ya tabbatar da cewa sojoji shida ne suka mutu a harin.

“Eh, mun yi rashin jami’ai abin takaici a ƙarshen mako a yankin Illela. Sai dai an tura ƙarin dakarun soja cikin gaggawa zuwa yankin, yayin da ake ci gaba da gudanar da ayyukan leƙen asiri domin gano da kuma kawar da ƴan ta’addan da suka aikata hakan.

“Kamar yadda al’adar soja ta tanada, ba za mu bayyana sunayen jarumanmu da suka rasu ba har sai an sanar da iyalansu.

“Saboda haka muna roƙon kafofin yaɗa labarai da su mutunta sirrin iyalan waɗanda abin ya shafa tare da kauce wa wallafa alƙaluman asara marasa tabbaci. Maimakon haka, ya kamata a mayar da hankali kan sadaukarwa da jajircewar dakarunmu,” in ji jami’in.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
Next Post
Ƴan Takarar Gwamna A Gombe Sun Yi Watsi Da Yunƙurin Pantami Na PDP

Ƴan Takarar Gwamna A Gombe Sun Yi Watsi Da Yunƙurin Pantami Na PDP

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026
'Yan Bindiga

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.