Wasu da ake zargin ƴan ta’addan Lakurawa ne sun kashe sojoji bakwai a wani kwanton ɓauna da suka yi a ƙauyen Runji, mai tazarar kusan kilomita 10 daga garin Illela a Ƙaramar Hukumar Illela ta Jihar Sakkwato.
Majiyoyin yankin sun ce lamarin ya faru ne a yammacin ranar Asabar da ta gabata yayin da dakarun ke dawowa daga wani samame da suka kai maɓoyar Lakurawa.
Mazauna yankin sun bayyana cewa sojojin sun kai hari sansanin ƴan ta’addan ne da motocin soja guda uku, wani farmaki da ake kyautata zaton ya jawo wa ƴan bindigar asara mai yawa.
Wata majiya da ta san yadda lamarin ya faru ta ce ɗaya daga cikin motocin sojojin ta samu matsalar inji yayin da suke komawa sansaninsu da ke Illela, lamarin da ya sa wasu daga cikin sojojin suka tsaya a gefen hanya domin gyara ta.
Da alama ƴan ta’addan sun tattaru tare da bibiyar sojojin domin ɗaukar fansa kan harin da aka kai musu a sansaninsu,” in ji majiyar.
Ta ƙara da cewa maharan sun iso yankin ne a kan babura kusan 30, inda kowane babur ke ɗauke da mayaƙa uku masu ɗauke da muggan makamai.
“Sun tarar da sojojin a wajen da ake gyaran motar, sannan aka yi musayar wuta mai tsanani na wani lokaci,” in ji majiyar.
Sai dai wani rahoto ya ce sojoji bakwai da farar hula ɗaya ne suka rasa rayukansu a harin kwanton ɓaunar.
“Bayan sojojin sun bar motar da ta lalace, suna tafiya zuwa sansaninsu tare da taimakon wani farar hula da ya san yankin sosai, sai Lakurawa suka yi musu kwanton ɓauna suka kashe sojojin bakwai da jagoransu na farar hula,” in ji majiyar.
Wani mazaunin Illela, wanda ya nemi a sakaya sunansa saboda dalilan tsaro, ya ce an fara tabbatar da mutuwar sojoji shida a wurin da lamarin ya faru, sannan daga baya aka gano gawar wani soja a cikin wani daji da ke kusa da wurin, wanda ya sa adadin ya kai bakwai.
“Mun ga gawarwaki bakwai a wurin, sannan aka sake gano wata gawar washegari,” in ji shi.
Majiyoyin tsaro ma sun tabbatar da harin, inda suka ce an kwashe gawarwakin sojojin da aka kashe zuwa Sakkwato.
Wani jami’in gwamnati a yankin ya kuma bayyana cewa wani babban jami’in soja mai muƙamin Laftanar a rundunar sojin Nijeriya na cikin waɗanda aka kashe a harin.
Kakakin rundunar ƴansandan Jihar Sakkwato, DSP Ahmad Rufa’i, da mai bai wa gwamna shawara kan harkokin tsaro, Kanal Ahmed Usman, sun ƙi yin tsokaci kan lamarin.
Sai dai wani babban jami’in soja da ya nemi a sakaya sunansa ya tabbatar da cewa sojoji shida ne suka mutu a harin.
“Eh, mun yi rashin jami’ai abin takaici a ƙarshen mako a yankin Illela. Sai dai an tura ƙarin dakarun soja cikin gaggawa zuwa yankin, yayin da ake ci gaba da gudanar da ayyukan leƙen asiri domin gano da kuma kawar da ƴan ta’addan da suka aikata hakan.
“Kamar yadda al’adar soja ta tanada, ba za mu bayyana sunayen jarumanmu da suka rasu ba har sai an sanar da iyalansu.
“Saboda haka muna roƙon kafofin yaɗa labarai da su mutunta sirrin iyalan waɗanda abin ya shafa tare da kauce wa wallafa alƙaluman asara marasa tabbaci. Maimakon haka, ya kamata a mayar da hankali kan sadaukarwa da jajircewar dakarunmu,” in ji jami’in.















Discussion about this post