ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji 7 A Harin Kwantan Ɓauna A Sakkwato

by Rabi'u Ali Indabawa
1 week ago

Wasu da ake zargin ƴan ta’addan Lakurawa ne sun kashe sojoji bakwai a wani kwanton ɓauna da suka yi a ƙauyen Runji, mai tazarar kusan kilomita 10 daga garin Illela a Ƙaramar Hukumar Illela ta Jihar Sakkwato.

Majiyoyin yankin sun ce lamarin ya faru ne a yammacin ranar Asabar da ta gabata yayin da dakarun ke dawowa daga wani samame da suka kai maɓoyar Lakurawa.

Mazauna yankin sun bayyana cewa sojojin sun kai hari sansanin ƴan ta’addan ne da motocin soja guda uku, wani farmaki da ake kyautata zaton ya jawo wa ƴan bindigar asara mai yawa.

ADVERTISEMENT

Wata majiya da ta san yadda lamarin ya faru ta ce ɗaya daga cikin motocin sojojin ta samu matsalar inji yayin da suke komawa sansaninsu da ke Illela, lamarin da ya sa wasu daga cikin sojojin suka tsaya a gefen hanya domin gyara ta.

Da alama ƴan ta’addan sun tattaru tare da bibiyar sojojin domin ɗaukar fansa kan harin da aka kai musu a sansaninsu,” in ji majiyar.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

Ta ƙara da cewa maharan sun iso yankin ne a kan babura kusan 30, inda kowane babur ke ɗauke da mayaƙa uku masu ɗauke da muggan makamai.

“Sun tarar da sojojin a wajen da ake gyaran motar, sannan aka yi musayar wuta mai tsanani na wani lokaci,” in ji majiyar.

Sai dai wani rahoto ya ce sojoji bakwai da farar hula ɗaya ne suka rasa rayukansu a harin kwanton ɓaunar.

“Bayan sojojin sun bar motar da ta lalace, suna tafiya zuwa sansaninsu tare da taimakon wani farar hula da ya san yankin sosai, sai Lakurawa suka yi musu kwanton ɓauna suka kashe sojojin bakwai da jagoransu na farar hula,” in ji majiyar.

Wani mazaunin Illela, wanda ya nemi a sakaya sunansa saboda dalilan tsaro, ya ce an fara tabbatar da mutuwar sojoji shida a wurin da lamarin ya faru, sannan daga baya aka gano gawar wani soja a cikin wani daji da ke kusa da wurin, wanda ya sa adadin ya kai bakwai.

“Mun ga gawarwaki bakwai a wurin, sannan aka sake gano wata gawar washegari,” in ji shi.

Majiyoyin tsaro ma sun tabbatar da harin, inda suka ce an kwashe gawarwakin sojojin da aka kashe zuwa Sakkwato.

Wani jami’in gwamnati a yankin ya kuma bayyana cewa wani babban jami’in soja mai muƙamin Laftanar a rundunar sojin Nijeriya na cikin waɗanda aka kashe a harin.

Kakakin rundunar ƴansandan Jihar Sakkwato, DSP Ahmad Rufa’i, da mai bai wa gwamna shawara kan harkokin tsaro, Kanal Ahmed Usman, sun ƙi yin tsokaci kan lamarin.

Sai dai wani babban jami’in soja da ya nemi a sakaya sunansa ya tabbatar da cewa sojoji shida ne suka mutu a harin.

“Eh, mun yi rashin jami’ai abin takaici a ƙarshen mako a yankin Illela. Sai dai an tura ƙarin dakarun soja cikin gaggawa zuwa yankin, yayin da ake ci gaba da gudanar da ayyukan leƙen asiri domin gano da kuma kawar da ƴan ta’addan da suka aikata hakan.

“Kamar yadda al’adar soja ta tanada, ba za mu bayyana sunayen jarumanmu da suka rasu ba har sai an sanar da iyalansu.

“Saboda haka muna roƙon kafofin yaɗa labarai da su mutunta sirrin iyalan waɗanda abin ya shafa tare da kauce wa wallafa alƙaluman asara marasa tabbaci. Maimakon haka, ya kamata a mayar da hankali kan sadaukarwa da jajircewar dakarunmu,” in ji jami’in.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi

June 1, 2026
NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
Tsaro

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

May 31, 2026
Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP
Tsaro

Yadda Muka Kashe Masu Garkuwa 4 Da Suke Shirin Kai Hari Kan Attajirai A Legas —CP

May 31, 2026
Next Post
Ƴan Takarar Gwamna A Gombe Sun Yi Watsi Da Yunƙurin Pantami Na PDP

Ƴan Takarar Gwamna A Gombe Sun Yi Watsi Da Yunƙurin Pantami Na PDP

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.