Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya sanar da rasuwar Mista Ifeanyi Izeze, ɗaya daga cikin mambobin farko na tawagar yaɗa labaransa.
Sanarwar rasuwar ta fito ne cikin wata takarda da mai ba Atiku shawara kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, ya fitar a ranar Lahadi. A cewar sanarwar, Izeze ya shiga tawagar yaɗa labaran Atiku a shekarar 2006 bayan ya bar kamfanin Aluminium Smelter Company of Nigeria da ke Ikot-Abasi, inda yake aiki a matsayin manajan ofis.
- Gwamnatin Kano Ta Rushe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi, Ta Haɗe Ta Da Ma’aikatar Ilimi
- Atiku Abubakar Ya Zargi Bola Tinubu Da Raunana Dimokuraɗiyya
Sanarwar ta ce marigayin ya kawo ƙwarewa mai yawa daga ɓangaren aikin jarida da kuma masana’antar mai da iskar gas, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen tsara dabarun yaɗa labarai da manufofin kamfen ɗin Atiku, musamman a yankin Neja Delta.
Ifeanyi Izeze ya yi karatun ilimin ƙasa (Geology) har zuwa matakin digiri na gaba a Jami’ar Fatakwal kafin daga baya ya koma aikin jarida. A lokacin aikinsa na jarida ya riƙa rubuce-rubuce kan harkokin mai da gas ga jaridu kamar Sunray Newspaper, Anchor Newspaper da NewAge Newspaper.
An san marigayin da barkwanci da kuma tsananin imani a addinin Kirista. Ya kasance limamin cocin Christ Embassy kuma mamba ne a Pentecostal Fellowship of Nigeria. Ya rasu ya bar ‘ya’ya da jikoki tare da yayansa, Emeka Izeze, wanda shahararren dan jarida ne da ke aiki da The Guardian Newspapers. Iyalansa ba su sanar da ranar jana’iza ba tukuna.















Discussion about this post