ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Waiwaye Adon Tafiya: Manyan Nasarorin Da Aka Cimma A Dangantakar Kasashen Afirka Da Sin A 2025

by Sulaiman
6 months ago
Afirka

Kyakkyawar dangantakar dake tsakanin kasashen Afirka da Sin kamar rana ce da ta kwallaro, babu wanda zai ce bai ganta ba sai makaho, ko shi ma makahon sai ya ji zafinta.

A shekarar 2025, hadin gwiwar Sin da Afirka ta sake samun muhimmin ci gaba ta hanyar ziyarar aiki ta diflomasiyya mai zurfi, zuba jari a manyan kayayyakin more rayuwa, da kuma hada hannu ta bangarori daban-daban kamar kimiyya da fasaha wanda hakan ke nuna ci gaba a daidaiton manufofi tsakanin bangarorin biyu.

Bari mu kawo wani dan takaitaccen bayani game da manyan ci gaba da aka cimma a hadin gwiwar Sin da Afirka a shekarar 2025, tare da warware zare da abawa kan abin da sabon ci gaban ke nunawa dangane da hadin gwiwar kasashen a nan gaba.

ADVERTISEMENT

 

Ziyarar aiki da ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi ya kawo Afirka

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

A ci gaba da al’adar fiye da shekaru 30, Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi ya ziyarci kasashen Afirka da dama a tsakanin 5-11 ga watan Janairun 2025 don sake tabbatar da dangantakar diflomasiyya da kuma binciko sabbin hanyoyin hadin gwiwa. Wannan ziyarar ta sake tabbatar da manufar ci gaba da cin moriyar juna a tsakanin bangarorin biyu.

 

Baje kolin tattalin arziki da ciniki na Sin da Afirka na hudu a Changsha

An gudanar da wannan taron baje kolin na hudu daga 12 zuwa 15 ga watan Yunin bana a Changsha, babban birnin lardin Hunan. Baje kolin ya tattaro kusan kamfanonin Sin da Afirka 4,700, kuma an baje kolin kayayyakin Afirka sama da 800 daga kasashe da dama.

An gudanar da taron ne tare da bikin cika shekaru 25 na taron dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC), wanda hakan ke jaddada tsarin ci gaba na dogon lokaci na ci gaba da huldar Sin da Afirka.

 

Fadada ciniki da katse shingen haraji zuwa sifili ga kasashen Afirka

A shekarar 2025, cinikayya tsakanin Sin da kasashen Afirka ta ci gaba da bunkasa sosai, cinikayyar Sin da Afirka a cikin watanni biyar na farko bayan katse shingen haraji ta karu da kashi 12.4% a shekara. Sin ta dakatar da haraji kashi 100 bisa 100 ga dukkan kasashen Afirka 53 wadanda suke da huldar diflomasiyya da kasar. Wannan manufar ta rage shingen ciniki sosai kuma ta inganta damar shiga kasuwa da fitar da kayayyaki daga Afirka. Wannan fadada manufofin ciniki ya nuna yadda aka sauya tsarin yarjejeniyar cinikayya daga yarjejeniya ta dan wani lokaci daya ko mai iyaka zuwa hadewar kasuwa mafi tsari kuma ta dogon lokaci.

 

Mu’amalar jama’a, al’adu, ilimi da bude ido

Tattaunawar Jama’a da Jama’a ta Afirka da Sin wacce ta gudana a watan Mayu na 2025 a Lusaka, Zambia, ta tattaro kungiyoyin jama’a, shugabannin kasuwanci, ‘yan kasuwa, da masu tsara manufofi daga Afirka da Sin. Ta jaddada hadin gwiwa tsakanin al’ummar bangarorin biyu fiye da yadda bangare daya kacal ke mu’amalarsa.

A irin wannan tattaunawar ta hadin gwiwa da ta gudana a wani taron hadin gwiwa na 2025 a birnin Jinhua na lardin Zhejiang, an sanya hannu kan wasu yarjejeniyoyi 33, wadanda suka shafi ciniki, saka hannun jari na kasashen waje, kwangilar injiniyanci, gina rumbunan ajiya a kasashen waje, wadanda darajarsu ta kai yuan biliyan 40.11 (kimanin dalar Amurka biliyan 5.63).

Bayan kasuwanci, taron Jinhua ya hada da musayar al’adu da yawon bude ido, inda aka gudanar da bikin baje kolin al’adu da yawon bude ido na Afirka na farko.

 

Hadin gwiwar kimiyya, fasaha da kirkire-kirkire da hukumar tarayyar Afirka

A watan Satumba na 2025, Hukumar Tarayyar Afirka (AUC) da Ma’aikatar Kimiyya da Fasaha ta Sin sun sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna don zurfafa hadin gwiwa a fannin kimiyya da fasaha. Daga 19-21 ga watan Nuwamban 2025 kuma, an gudanar da taron hadin gwiwa kan ci gaban kirkire-kirkire na Sin da Afrika a birnin Wuhan, da nufin daidaita hadin gwiwar kimiyya da fasaha kan bukatun ci gaban Afirka, ciki har da makamashi mara cutar da muhalli (green energy), biranen kimiyya, ci gaba mai dorewa, da sauransu.

 

Hadin gwiwar fasaha a ɓangaren kula da muhalli

Cibiyar Hadaka ta Sin da Afirka mai Amfani da Tauraron Dan Adam (CACSA), ta fadada hadin gwiwarta da Afirka a shekarar 2025. Tun kafuwarta a shekarar 2023, ta rattaba hannu kan wasu yarjejeniyoyi da kasashen Afirka 16, inda ta kafa na’urori 14 na kula da sararin samaniya masu amfani da tauraron dan adam wadanda ke tallafawa sama da hotuna 70,000 masu inganci daga hangen nesa. Wannan yana tallafawa tsare-tsaren birane, sa ido kan yadda ake amfani da kasa, kula da tekuna ko koguna, sa ido kan muhalli, da sauransu.

Ta hanyar shirye-shirye a fannin kimiyya, samar da makamashi mara cutarwa ga muhalli, da kayayyakin more rayuwa na dijital, Sin da Afirka suna zurfafa hadin gwiwa ba wai kawai a fannin kayayyakin more rayuwa da aka fi sani kamar hanyoyi, layin dogo, tashoshin jiragen ruwa ba, har ma a fannoni masu muhimmanci na “zamani” da karni na 21 ke bukata don ci gaba.

 

Masu karatu, mu tambayi kanmu mana, me wannan gagaruman sabbin nasararorin hadin gwiwar Afirka da Sin ke nufi a nan gaba?

Daga cinikayya, da samar da ababen more rayuwa zuwa hadin gwiwa na dabarun fasaha da zamantakewa ta zamani da suka hada da kimiyya da fasaha, tattalin arzikin dijital, samar da makamashi mara cutarwa ga muhalli, da kirkire-kirkire. Hakan yana nuna ci gaba daga hadin gwiwa mai karfi irin na baya zuwa ga hadin gwiwa mai fadi a bangarori daban-daban na zamani, masu amfanarwa ga juna. Yarjejeniyar Kimiyya da kirkire-kirkire ta 2025 tare da Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) da hadin gwiwar CACSA shaida ne na wannan ci gaban sauyin.

Idan aka aiwatar da wadannan yarjejeniyoyin hadin gwiwar yadda ya kamata, wannan hadin gwiwa mai zurfi zai iya taimakawa Afirka wajen hanzarta gyara da ci gaban masana’antunta da komawa cikin zamani. Har ila yau, hakan zai sanya Sin da Afirka a matsayin abokan tarayya wajen tsara sabon tsarin ci gaban duniya mai bangarori daban-daban.

 

 

 

 

 

 

 

 

Afirka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
  • Sulaiman
    Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

MASU ALAKA

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya
Ra'ayi Riga

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

June 5, 2026
Next Post
Me Ya Sa Ya Kamata Kasashen Afirka Su Bunkasa Tattalin Arziki Tare Da Kare Muhalli?

Me Ya Sa Ya Kamata Kasashen Afirka Su Bunkasa Tattalin Arziki Tare Da Kare Muhalli?

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.