Yayin zaman kwamitin sulhu na MDD na jiya Laraba, an ci gaba da muhawarar da ba a kammala ba a ranar 27 ga wata bisa jigon “Tsaro da kare hanyoyin ruwa a yankunan teku”.
A lokacin zaman na jiya, wakilin kasar Japan ya yi ta karawa batutuwan tekun gabashin Sin da tekun kudancin Sin gishiri, ya kuma zargi Sin da manufofinta na tsaro, da kuma halin da ake ciki a mashigar tekun Taiwan.
Dangane da haka, nan take wakilin Sin ya karyata kalaman, kuma ya nuna cewa, jerin ayyuka masu hadari da Japan ke aikatawa a fannin tsaro a baya-bayan nan, sun karyata yadda Japan ke kiran kanta da “kasa mai zaman lafiya”, da kuma manufarta ta “kayyade karfin soja don kare kai kadai”.
A jawabinsa babban jami’in tawagar dindindin ta kasar Sin a MDD Teng Fei, ya ce ba shakka kasar Japan tana gaggawar kara karfin sojanta, kuma ta riga ta dauki wasu matakai na ainihi game da hakan.
Teng ya kara da cewa, dole ne Japan ta yi tunani, game da ko za ta ci gaba da barin cutar ra’ayin fin karfin soja ta ci gaba da yaduwa, ko kuwa za ta yi nadama kan laifuffukan yakin mamaya, ta kuma samu amincewar kasashe makwabta a Asiya da ma daukacin al’ummun kasa da kasa.
Bugu da kari, a wannan rana, a jawabin mayar da martani karo na 2, na babban taron duba tsarin hana yaduwar makaman nukiliya karo na 11, tawagar Sin ta nuna cewa, tun bayan hawan gwamnatin firaminista Takaichi Sanae kan karagar mulki, batun mallakar makaman nukiliya na Japan ba wai barazana ce kadai ba, domin a daya bangaren hakan na haifar da babban kalubale ga tsarin kasa da kasa na bayan Yakin Duniya na Biyu, da kuma tsarin hana yaduwar makaman nukiliya. (Amina Xu)















Discussion about this post