Yayi da a kasar nan ake kokarin magance wata matsala, sai kuma aga wata sabuwar matsalar ta kara kunno kai, wannan lamarin, za a iya cewa, ya yi daidai da batun kisan gillar da aka yi wa wani mai yi wa kasa hidima mai suna Ben Agir.
Ana dai zargin wasu ‘yan kungiyar Kwato da Gora ne, suka hallaka marigayin ne, a yankin Mbajor da ke a karamar hukumar Buruku, ta jihar Biniwe, inda kisan ya nuna a zahiri, ba batun ana kan wani kokarin, dakile wata matsalar, sai kuma wata ta bulla.
Jihar ta Biniwe dai, na ci gaba da fuskantar matsalar hare-haren ‘yan bindiga musamman a wasu kauyukan ta hanyar cin galaba a kan jami’an tsaro da aka girke, a yankunan da hare- haren ke yin kamari.
Kazalika, jihar ta kasance akwai jami’in tsaro iri-iri kamar ‘yansanda jami’ain sibil difens, jami’an tsaro na farin kaya wato DSS, wadanda aka ba za su, zuwa kananan hukumomin jihar, bisa nufin tabbatar da tsaro.
Amma abin bakin cikin, shi ne, yadda ake ta ci gaba da samun yawan hare-haren na ‘yan bindiga a yankunan jihar, na ci gaba da jefa fargaba, da kuma tayar da hankulan alummomin da ke a yankunan, wanda a zahiri, hakan ke nuna cewa, ana samun gibin gazawar samun bayanan sirri.
An dai kafa jami’an na ‘yan Kato da Gora ne, bisa nufin rage kalubalen na rashin tsaro, amma abin takaici, sai aka buge da ana zargin wasun su da azabtar da mutanen da ba su ji, ba su kuma gani ba da yawan yin kame da kuma karbar cin hanci, a gun wadanda suka kama.
Shin bisa irin wannan mummunar dabi’ar ta ‘yan Kato da Gora, me ke nan za a iya cewa, kasar ta amfana da shi?
Bugu da kari, bisa wannan dabi’ar ta su, a kan alumomin, za a iya cewa, horon da aka ba su domin gudanar da aikinsu na samar da tsaro, ya tafi a banza, musamman ganin yadda suke wuce Makadi da Rawa, na ka’idar da aka gindaya masu, na ayyukansu na bayar da tsaro, ga alumma.
‘Yan da dama, musamman a yankunan karkara, na ci gaba da fuskantar barazana daga gun ‘yan Kato da Gora, wadanda a zahiri, an kafa su ne, da nufin kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
Marigayi Ben dai, an tura shi zuwa jihar Gombe ne, domin yiwa kasar hidima.
Rahotannin sun ce, ‘yan Kato da Gorar, sun hallaka marigayin ne, bayan sun kama, bisa zarginsa da satar wani Babur, inda suka lakada masa na Jiki, har ta kai ga, ya fita daga cikin hayyacinsa.
An ji ma ace, Ben ya sace Babur din ne, amma mai ya kai ‘yan Kato da Goran, aikata masa wannan danyen hukuncin da har ta kai gay a rasa ransa?
Bugu da kari, shin wane irin horo ne, aka bai wa ‘yan Kato da Goran, da har za su rinka daukar doka a hannunsu?
Hakazalika, irin makamancin wannan yanayin ya faru a watan Agustan 2025, yayin da gungun wasu ‘yan Kato da Gora, a jihar Anambara suka kutsa, a cikin masaukin Oba, na Idemili, a karamar hukuma ta Kudu, suka lallasa wata mai yi wa kasa hidima, mai suna Jennifer Elohor.
Sai dai, gwamnatin jihar, daga baya ta kore su daga aiki tare da gurfanar da su, a gaban kotu, inda a yanzu, suke ci gaba da fuskantar tuhuma.
Karin wani abin takaicin shi ne, a yayin da Jennifer ke dakon samakamakon huncin da kotun za ta yanke wa ‘yan Kato da Goran da suka aikata mata ta’asar sai kuma aka samu bullar wani sabon lamarin na kisan gillar da aka yiwa marigayi Ben a jihar Biniwe.
A Nijeriyar mu ta yau dai, a bayyane yake yadda masu kayan Sarki, ke yin amfani da karfin ikonsu, suna gallaza wa jama’a. Misali, a lokacin zanga-zangar #ENDSARS, wasu ‘yansanda sun yi amfani da karfin Tuwo wajen tumurmusa wasu masu gudanar da zanga-zangar ta #ENDSARS, wanda hakan ya sanya akaita ta kai komin, ganin an haramta rundunar ta #ENDSARS, daga baya kuma aka samu nasarar yin hakan.
Lokaci dai ya yi ga daukacin matakan gwamnati uku na kasar takawa ‘yan Kato da Gora da kuma suran jami’an tsaron kasar, kan take ‘yancin ‘yan Adam.
Ya zama wajbi. Jami’an tsaro a kasar nan su kwan da sanin cewa, an kafa su ne, domin kare rayukan ‘yan kasar amma ba wai daukar rayukansu bisa zalunci ba
Kazalika, dole ne, ‘yan Kato da Gora da ke a jihar ta Biniwe da sauran wadanda ke sauran sassan kasar nan da su sani cewa, an kafa su ne, domin wanzar da aikin zaman lafiya da kare rayukan ‘yan Nijeriya da dukiyoyinsu.
Muna mika ta’aziyyar mu ga iyayen marigayi ben, da kuma hukumar ta NYSC ta kasa, bisa wannan rashin da a yi.
A ra’ayin wannan Jaridar, ba tare da bata wani lokaci ba, gwamnatin jihar Biniwe, ta tabbatar da an hukunta ‘yan Kato da Goran da ake zargin da aikata wannan mummunar ta’asar ga Ben.
Haka, ya zama wajbi, a san irin horon da za a rinka bai wa ‘yan Kato da Goran tare da kuma sanya ido a kansu, musamman domin kaucewa hallaka jama’a, ba gaira ba sabat.















Discussion about this post