Jiya Laraba, shugaban sashen kula da harkokin soja na ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Sun Xiaobo, ya ba da jawabi a yayin taron nazarin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya karo na 11, wanda ake gudanarwa a hedkwatar MDD dake birnin New York.
Cikin jawabinsa, Sun ya bayyana cewa, ra’ayin babakere, da karfin siyasa na tilastawa wani, da kuma matakin kashin kai da wani bangare ke dauka, sun kasance ainihin barazana ga yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya.
Ya kuma kara da cewa, ya kamata kasashen duniya su hada kansu domin nuna kiyayya ga wadanda suke son daukar matakan soja, ko kuma suke barazanar daukan matakan soja a dangantakar dake tsakanin kasa da kasa, tare da karfafa aniyar kasashen duniya ta yin rigakafin yaki na makaman nukiliya.
Kana, kasar Sin ta yi kira ga kasashen dake da makaman nukiliya da su nuna karfin siyasa, domin gaggauta kulla yarjejeniyar hana wata kasa kasancewa ta farko da za ta yi amfani da makaman nukiliya ta hanyar gudanar da shawarwari, ko kuma gabatar da sanarwar siyasa game da hakan.
Ban da haka kuma, tawagar wakilan kasar Sin ta bayyana cewa, cikin shekaru 20 da suka gabata, kasar Amurka ta janye jiki daga yarjejeniyoyin kayyade makamai da dama, tana kuma ci gaba da gurgunta yanayin tsaron kasashen duniya, da tsarin kayyade makaman nukiliya.
Alal hakika dai, kasar Amurka ita ce asalin mai bata tsarin kayyade makaman nukiliya da zaman karko na manyan tsare-tsare. (Mai Fassara: Maryam Yang)















Discussion about this post