ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanda Ya Sa Takalma Ya San Ko Ya Dace Ko A’a

by CGTN Hausa
2 years ago
takalma

“Mataki ne mai burgewa”, in ji Miriam Akpan, ma’aikaciyar gwamnati a Nijeriya wadda ta nuna yabo ga layin dogo na Abuja bayan da ta hau jirgin, layin dogon da aka kaddamar da ita a hukumance a kwanan baya. Miriam Akpan ta ce, “Jirgin yana da dadi, kuma an tafiyar da tashoshin jirgin yadda ya kamata. Yanzu kudin da na kashe wajen zirga-zirga tsakanin gida da ofis ya ragu sosai, ga shi kuma jirgin ya fi sauri idan an kwatanta da mota wadda ta kan samu cunkuso, gaskiya na ji dadi.” 

Mustapha Bello, dalibi ne daga jami’ar Abuja, wanda shi ma ya ji dadin tafiya ta layin dogon, ya kuma yi fatan za a fadada layin dogo har zuwa bayan garin da yake zama, ya ce, “tafiya ce mai dadi, kuma ina fatan layin dogon zai taimaka ga saukaka harkokin zirga-zirga ga mazauna birnin, baya ga kyautata tattalin arziki da zaman al’umma.”

  • An Tafka Gumurzu, Sojoji Sun Kashe Ƴan Boko Haram Da Yawa, Wasu Sun Miƙa Wuya
  • Sadaukar Da Kai Ga Hidimtawa Jama’a: Tasirin Mahaifin Xi Jinping A Kan Dansa

Kamfanin kasar Sin ne ya gina layin dogon na Abuja, wanda ya kasance layin dogo na farko da aka shimfida a birnin, wanda kuma ya kasance wata babbar nasara da aka samu sakamakon aiwatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”. An ce, layin dogon na da tsawon kilomita 45, kuma bayan da aka kaddamar da shi a hukumance, zai yi matukar saukaka matsalar cunkuson mota da ake fuskanta a birnin, wanda baya ga hakan, zai kuma rage kudin zirga-zirga ga mazauna birnin, tare da bunkasa tattalin arziki da zaman al’umma a sassan da layin dogon ya ratsa, wanda har zai haifar da babban tasiri ga bunkasuwar layukan dogo a biranen kasashen yammacin Afirka da ma na Afirka baki daya.

ADVERTISEMENT

Hasali ma dai, cikin shekaru 10 da aka gabatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, kasar Sin ta daddale takardun yarjejeniyoyin hadin gwiwa sama da 200 tare da kasashen duniya sama da 150 da ma kungiyoyin kasa da kasa fiye da 30, shawarar da ta samar da dandalin hadin gwiwa mafi girma a tsakanin kasa da kasa, wadda kuma ta samar da hakikanan alfanu ga jama’ar kasashen da suka karbi shawarar, kuma layin dogo na Abuja wani misali ne kawai na nasarorin da aka cimma sakamakon aiwatar da shawarar.

Duk da haka, ko irin wannan hadin gwiwar da ke haifar da alfanu ma Amurka da sauran kasashen yamma na shafa masa bakin fenti, inda shugaban kasar Amurka Joe Biden a yayin da ya tattauna tare da dan jarida a kwanakin baya, ya bayyana shawarar a matsayin “shirin da ake kyamarsa”, ya kuma kara da cewa, “A duba me ke faruwa a Afirka”.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Haka ne, a duba me ke faruwa a Afirka. Sakamakon shawarar “ziri daya da hanya daya”, kasashen Afirka da dama sun samu tagwayen hanyar mota ta farko, da ma gadar ketare teku ta farko da ma yankin masana’antu na farko, baya ga cibiyar kandagarkin cututtuka mai ingantattun kayayyakin aiki ta farko da ta game ko ina a nahiyar Afirka, da gaske ne shawarar ta samar da manyan sauye-sauye ga kasashen Afirka.

Sinawa kan ce, sai wanda ya sa takalma ya san ko ta dace ko a’a. Abin hakan yake, sai kasashen da suka aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya suke iya magana a kanta. Shugaban tarayyar Nijeriya Bola Tinubu a yayin da ya halarci bikin kaddamar da layin dogon, ya bayyana shi a matsayin “hanya mai kyakkyawar makoma da za ta taimakawa Nijeriya inganta ababen zirga-zirga da ma bunkasa tattalin arziki da zaman al’umma”, da kuma “alama ta dauwamammen ci gaban Nijeriya”, furucin da ya bayyana ma’anar shawarar ga kasashen da suka karbe ta.

Abu ne mai sauki a yi wa wasu suka, sai dai, da wuya a iya yin wani abu da ya zarce na wasu kyau. Kasar Sin na son ganin kasa da kasa su aiwatar da hadin gwiwar cin moriyar juna tare da kasashen Afirka cikin daidaito, don su samar da hakikanin taimako ga bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma na kasashen Afirka. Muna kuma fatan ganin Amurka ta samar da kudaden jari, don ta samar da hakikanin gudummawa wajen raya kasashen Afirka. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

takalma
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Gobara Ta Tashi A Kantin Shoprite Da Ke Kano

Gobara Ta Tashi A Kantin Shoprite Da Ke Kano

LABARAI MASU NASABA

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.