ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wane Irin Tasiri Ya Kamata Babbar Kasa Ta Samar Wa Duniya?

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Duniya

Kasar Sin da kasar Najeriya dukkansu manyan kasashe ne. Sai dai wane irin tasiri ya kamata wata babbar kasa ta samar wa duniya?

A zamanin da muke ciki, wasu manyan kasashe na son nuna karfinsu, ta hanyar cin zarafin sauran kasashe. Na san wannan abun da suke yi, galibin mutanen duniya ba za su yarda da shi ba.

Hausawa su kan ce, babba juji ne. Da wannan karin magana ake nufin cewa, ya kamata a bari mai karfi ya dauki karin nauyi. To, wannan tunani ya zama dai-dai da na Sinawa. Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya taba bayyana cewa, ya kamata manyan kasashe su nuna cikakken karamci, da kokarin sauke nauyin dake bisa wuyansu.

ADVERTISEMENT

Kyan alkawari cikawa. Wani abun da ya faru jiya ya shaida yadda kasar Sin ke kokarin cika alkawarinta. An ce, a birnin Yaounde na kasar Kamaru, an shirya taron tattauna batun “shirin kasar Sin” karo na 14 a karkashin laimar kungiyar ciniki ta duniya (WTO). Inda wannan shiri ya shafi yin amfani da kudin da kasar Sin ta bayar, wajen ba da taimako ga kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki, don ganin sun halarci tsarin WTO tare da samun alfanu.

Duk a wajen taron, ministan kasuwancin kasar Sin, Wang Wentao, da babbar daraktar kungiyar WTO Ngozi Okonjo-Iweala, sun sa hannu kan yarjejeniyar sabunta “shirin kasar Sin”. Kana a cewar jami’in na Sin, kasar a ko da yaushe kasar Sin tana goyon bayan kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen dake nahiyar Afirka, don su ci gajiyar tsarin kasuwanci da ya shafi bangarori daban daban, da more damammakin da kasuwannin kasar Sin suke samarwa, ta hanyar fitar da karin kayayyaki zuwa kasar.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Hakika kasar Sin har kullum tana neman ganin ci gaban tattalin arzikin kasashe daban daban na bai daya, kana ta samar da dimbin taimako ga kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki, wadanda suka kunshi kasashe 33 dake nahiyar Afirka. Misali, a fannin cinikayya, tun daga ranar 1 ga watan Disamban shekarar 2024, kasar Sin ta aiwatar da manufar yafe dukkan harajin kwastam da ake karba kan kayayyakin da ake shigar da su kasar Sin daga kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki. Kafin daga bisani, kasar ta sanar da habaka tasirin manufar zuwa dukkan kasashe 53 dake nahiyar Afirka da suka kulla huldar diflomasiyya da kasar ta Sin, matakin da zai fara aiki a farkon watan Mayun bana.

Ban da haka, kasar Sin ta dauki matakan saukaka wa kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki hada-hadar ciniki da Sin, ciki har da yin amfani da dimbin bukukuwan ciniki da Sin take shiryawa, wajen tallar kayayyakin wadannan kasashen ga jama’ar kasar Sin.

Sa’an nan a fannin masana’antu, kasar Sin tana kokarin zuba karin jari a kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki. Inda a nahiyar Afirka, ake ganin yadda kamfanonin kasar ta Sin ke bude karin masana’antu a cikin yankunan raya tattalin arziki da ciniki da aka kafa a kasashen Afirka, wadanda suka shafi sarrafa amfanin gona, da kera kayayyakin gida masu amfani da lantarki, da jigilar kayayyaki, da sabon makamashi, da dai sauransu.

Ta wadannan misalai, muna iya ganin sahihancin kasar Sin a fannin ba da taimako ga kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki. Sai dai me ya sa kasar ta sha bamban da wasu kasashen dake yammacin duniya a wannan fanni? Me ya sa take kokarin ba da taimako, yayin da wasu kasashe ke neman cin zarafin saura? Dalili shi ne, tun tuni kasar Sin ta sanya burin kafa al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya a duniya, ta yadda za a tabbatar da ci gaban tattalin arzikin dukkan kasashe, da hadin gwiwar al’ummunsu, da wanzar da zaman lafiya a ko ina a duniyarmu. (Bello Wang)

Duniya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Duniya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 5 A Sokoto Da Zamfara, Sun Ƙwato Makamai

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.