ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wane Irin Tasiri Ya Kamata Babbar Kasa Ta Samar Wa Duniya?

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Duniya

Kasar Sin da kasar Najeriya dukkansu manyan kasashe ne. Sai dai wane irin tasiri ya kamata wata babbar kasa ta samar wa duniya?

A zamanin da muke ciki, wasu manyan kasashe na son nuna karfinsu, ta hanyar cin zarafin sauran kasashe. Na san wannan abun da suke yi, galibin mutanen duniya ba za su yarda da shi ba.

Hausawa su kan ce, babba juji ne. Da wannan karin magana ake nufin cewa, ya kamata a bari mai karfi ya dauki karin nauyi. To, wannan tunani ya zama dai-dai da na Sinawa. Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya taba bayyana cewa, ya kamata manyan kasashe su nuna cikakken karamci, da kokarin sauke nauyin dake bisa wuyansu.

ADVERTISEMENT

Kyan alkawari cikawa. Wani abun da ya faru jiya ya shaida yadda kasar Sin ke kokarin cika alkawarinta. An ce, a birnin Yaounde na kasar Kamaru, an shirya taron tattauna batun “shirin kasar Sin” karo na 14 a karkashin laimar kungiyar ciniki ta duniya (WTO). Inda wannan shiri ya shafi yin amfani da kudin da kasar Sin ta bayar, wajen ba da taimako ga kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki, don ganin sun halarci tsarin WTO tare da samun alfanu.

Duk a wajen taron, ministan kasuwancin kasar Sin, Wang Wentao, da babbar daraktar kungiyar WTO Ngozi Okonjo-Iweala, sun sa hannu kan yarjejeniyar sabunta “shirin kasar Sin”. Kana a cewar jami’in na Sin, kasar a ko da yaushe kasar Sin tana goyon bayan kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen dake nahiyar Afirka, don su ci gajiyar tsarin kasuwanci da ya shafi bangarori daban daban, da more damammakin da kasuwannin kasar Sin suke samarwa, ta hanyar fitar da karin kayayyaki zuwa kasar.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

Hakika kasar Sin har kullum tana neman ganin ci gaban tattalin arzikin kasashe daban daban na bai daya, kana ta samar da dimbin taimako ga kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki, wadanda suka kunshi kasashe 33 dake nahiyar Afirka. Misali, a fannin cinikayya, tun daga ranar 1 ga watan Disamban shekarar 2024, kasar Sin ta aiwatar da manufar yafe dukkan harajin kwastam da ake karba kan kayayyakin da ake shigar da su kasar Sin daga kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki. Kafin daga bisani, kasar ta sanar da habaka tasirin manufar zuwa dukkan kasashe 53 dake nahiyar Afirka da suka kulla huldar diflomasiyya da kasar ta Sin, matakin da zai fara aiki a farkon watan Mayun bana.

Ban da haka, kasar Sin ta dauki matakan saukaka wa kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki hada-hadar ciniki da Sin, ciki har da yin amfani da dimbin bukukuwan ciniki da Sin take shiryawa, wajen tallar kayayyakin wadannan kasashen ga jama’ar kasar Sin.

Sa’an nan a fannin masana’antu, kasar Sin tana kokarin zuba karin jari a kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki. Inda a nahiyar Afirka, ake ganin yadda kamfanonin kasar ta Sin ke bude karin masana’antu a cikin yankunan raya tattalin arziki da ciniki da aka kafa a kasashen Afirka, wadanda suka shafi sarrafa amfanin gona, da kera kayayyakin gida masu amfani da lantarki, da jigilar kayayyaki, da sabon makamashi, da dai sauransu.

Ta wadannan misalai, muna iya ganin sahihancin kasar Sin a fannin ba da taimako ga kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki. Sai dai me ya sa kasar ta sha bamban da wasu kasashen dake yammacin duniya a wannan fanni? Me ya sa take kokarin ba da taimako, yayin da wasu kasashe ke neman cin zarafin saura? Dalili shi ne, tun tuni kasar Sin ta sanya burin kafa al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya a duniya, ta yadda za a tabbatar da ci gaban tattalin arzikin dukkan kasashe, da hadin gwiwar al’ummunsu, da wanzar da zaman lafiya a ko ina a duniyarmu. (Bello Wang)

Duniya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Duniya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • Sulaiman
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

MASU ALAKA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata
Ra'ayi Riga

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

June 17, 2026
Next Post
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 5 A Sokoto Da Zamfara, Sun Ƙwato Makamai

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.