ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wane Irin Tasiri Ya Kamata Babbar Kasa Ta Samar Wa Duniya?

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Duniya

Kasar Sin da kasar Najeriya dukkansu manyan kasashe ne. Sai dai wane irin tasiri ya kamata wata babbar kasa ta samar wa duniya?

A zamanin da muke ciki, wasu manyan kasashe na son nuna karfinsu, ta hanyar cin zarafin sauran kasashe. Na san wannan abun da suke yi, galibin mutanen duniya ba za su yarda da shi ba.

Hausawa su kan ce, babba juji ne. Da wannan karin magana ake nufin cewa, ya kamata a bari mai karfi ya dauki karin nauyi. To, wannan tunani ya zama dai-dai da na Sinawa. Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya taba bayyana cewa, ya kamata manyan kasashe su nuna cikakken karamci, da kokarin sauke nauyin dake bisa wuyansu.

ADVERTISEMENT

Kyan alkawari cikawa. Wani abun da ya faru jiya ya shaida yadda kasar Sin ke kokarin cika alkawarinta. An ce, a birnin Yaounde na kasar Kamaru, an shirya taron tattauna batun “shirin kasar Sin” karo na 14 a karkashin laimar kungiyar ciniki ta duniya (WTO). Inda wannan shiri ya shafi yin amfani da kudin da kasar Sin ta bayar, wajen ba da taimako ga kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki, don ganin sun halarci tsarin WTO tare da samun alfanu.

Duk a wajen taron, ministan kasuwancin kasar Sin, Wang Wentao, da babbar daraktar kungiyar WTO Ngozi Okonjo-Iweala, sun sa hannu kan yarjejeniyar sabunta “shirin kasar Sin”. Kana a cewar jami’in na Sin, kasar a ko da yaushe kasar Sin tana goyon bayan kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen dake nahiyar Afirka, don su ci gajiyar tsarin kasuwanci da ya shafi bangarori daban daban, da more damammakin da kasuwannin kasar Sin suke samarwa, ta hanyar fitar da karin kayayyaki zuwa kasar.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Hakika kasar Sin har kullum tana neman ganin ci gaban tattalin arzikin kasashe daban daban na bai daya, kana ta samar da dimbin taimako ga kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki, wadanda suka kunshi kasashe 33 dake nahiyar Afirka. Misali, a fannin cinikayya, tun daga ranar 1 ga watan Disamban shekarar 2024, kasar Sin ta aiwatar da manufar yafe dukkan harajin kwastam da ake karba kan kayayyakin da ake shigar da su kasar Sin daga kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki. Kafin daga bisani, kasar ta sanar da habaka tasirin manufar zuwa dukkan kasashe 53 dake nahiyar Afirka da suka kulla huldar diflomasiyya da kasar ta Sin, matakin da zai fara aiki a farkon watan Mayun bana.

Ban da haka, kasar Sin ta dauki matakan saukaka wa kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki hada-hadar ciniki da Sin, ciki har da yin amfani da dimbin bukukuwan ciniki da Sin take shiryawa, wajen tallar kayayyakin wadannan kasashen ga jama’ar kasar Sin.

Sa’an nan a fannin masana’antu, kasar Sin tana kokarin zuba karin jari a kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki. Inda a nahiyar Afirka, ake ganin yadda kamfanonin kasar ta Sin ke bude karin masana’antu a cikin yankunan raya tattalin arziki da ciniki da aka kafa a kasashen Afirka, wadanda suka shafi sarrafa amfanin gona, da kera kayayyakin gida masu amfani da lantarki, da jigilar kayayyaki, da sabon makamashi, da dai sauransu.

Ta wadannan misalai, muna iya ganin sahihancin kasar Sin a fannin ba da taimako ga kasashe mafiya fama da koma bayan tattalin arziki. Sai dai me ya sa kasar ta sha bamban da wasu kasashen dake yammacin duniya a wannan fanni? Me ya sa take kokarin ba da taimako, yayin da wasu kasashe ke neman cin zarafin saura? Dalili shi ne, tun tuni kasar Sin ta sanya burin kafa al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya a duniya, ta yadda za a tabbatar da ci gaban tattalin arzikin dukkan kasashe, da hadin gwiwar al’ummunsu, da wanzar da zaman lafiya a ko ina a duniyarmu. (Bello Wang)

Duniya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Duniya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 5 A Sokoto Da Zamfara, Sun Ƙwato Makamai

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.