Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya tattauna ta wayar tarho da mataimakin firaminista, kuma ministan harkokin wajen Pakistan, Ishaq Dar, jiya Litinin.Dar ya yi cikakken bayani game da kokarin da bangaren Pakistan ke yi na yin sulhu tsakanin Iran da Amurka don tattaunawa, kuma ya gode wa bangaren Sin kan kokarinsa na kawo zaman lafiya.Wang Yi ya yaba wa bangaren Pakistan bisa gudanar da jagoranci mai adalci da daidaito kan tsagaita wuta tsakanin Iran da Amurka na wucin- gadi da kuma shirya taron tattaunawa a Islamabad.
Wang Yi ya bayyana cewa, a halin yanzu yanayin cimma tsagaita bude wuta yana da rauni sosai, kuma yanayin yankin yana cikin wani muhimmin lokaci mai sarkakiya.
Babban abin da ake bukata a gaggauce shi ne a yi iyakacin kokarin hana sake barkewar yaki, da kuma wargajewar neman tsagaita bude wuta da aka samu cikin wahala. Ya kamata al’ummun kasa da kasa su ci gaba da kara kokarin inganta zaman lafiya da tattaunawa, tare da nuna adawa a fili ga duk wani mataki na rushe tsagaita bude wuta da kuma kara tsananta kiyayya da juna.
Kazalika ya ce, bangaren Sin yana farin cikin ganin bangaren Pakistan ya taka rawar gani, kuma yana fatan shi da sauran al’ummun kasa da kasa da su hada da bangaren Pakistan, za su ci gaba da bayar da gudunmawa mai kyau don maido da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Gabas ta Tsakiya cikin gaggawa. (Amina Xu)















Discussion about this post