ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Abu Ya Sa Afirka Ta Zama Abin Koyi

by CMG Hausa
4 years ago
Afirka

Yau 18 ga watan Yuli rana ce da MDD ta kebe don tunawa da Nelson Mandela.

Idan an ba ni damar takaita ruhin marigayi Mandela da kalma daya, zan zabi “Hakuri”. Saboda ya taba bayyana cewa, “Lalata abu na da sauki, amma wanda ya dukufa wajen tabbatar da zaman lafiya shi ne jarumi.”

  • Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-3 Na Kasar Sin Ya Rabu Da Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

A sabili da ruhinsa na hakuri, bayan da Mandela ya kammala zamansa na shekaru 28 a gidan kurkuku, kuma ya zama shugaban kasa bakar fata na farko a tarihin kasar Afirka ta Kudu, bai nemi yin ramuwar gayya ga mutanen da suka taba cin zarafinsa ba.

ADVERTISEMENT

Don neman ganin an kafa wata sabuwar kasa, da samun sulhu tsakanin kabilu daban daban na kasar, ya nuna hakuri ga ‘yan kasarsa fararen fata, ta yadda a karshe dai ya cimma burin kare hakkin bakaken fata da kuma tabbatar da zaman daidaito a tsakaninsu da fararen fata.

A sauran kasashen Afirka ma, muna iya ganin yadda ra’ayi na hakuri ke taka muhimmiyar rawa. Misali a kasar Rwanda. Bayan abkuwar kisan kiyashi a shekarar 1994, wanda ya haddasa mutuwar mutane miliyan 1 a kasar, ba a ga wata ramuwar gayya daga ‘yan kabilar Tutsi ba. Maimakon haka, abun da aka yi shi ne neman samun maslaha. Cikin ‘yan kabilar Hutu dubu 120 da suka sa hannun kisan kiyashin, ban da yanke hukuncin kisa kan wasu mutane 90 da suka fi taka rawar aikata laifukan, sauran sun samu damar gyara halinsu. Hakurin da aka nuna ya tabbatar da kwanciyar hankali da hadin kan al’umma, inda wannan yanayi ya sa kasar kiyaye saurin karuwar tattalin arzinta na kashi 70% ko fiye da haka, tun bayan shekarar 2003.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Abin takaici shi ne, ra’ayi na hakuri da marigayi Mandela da sauran ‘yan Afirka ke da shi, har yanzu bai yi tasiri a wasu wurare ba, musamman ma babbar kasar da take daukar kanta a matsayin mai kare dimokuradiya da hakkin dan Adam.

A wannan kasa ra’ayin bambancin launin fata ya zama ruwa dare, inda yiwuwar ‘yan sanda su kama bakar fata ta ninka ta farar fata har sau 6. Kana an taba ganin yadda wani dan sanda ya danne wuyan wani saurayi bakar fata da gwiwa, har ya kashe shi, da yadda ‘yan sanda suka bindige wani bakar fata da ba shi da makami, wanda har aka samu raunukan bindigogi 60 a jikinsa, al’amuran da suka sanya al’ummar duniya cikin kaduwa.
Wannan kasa, ko da yake tana da karfi sosai a fannonin tattalin arziki da kimiyya da fasaha, amma tana ci gaba da fama da yanayi na koma baya, ta fuskar zaman daidaito a tsakanin al’umma, da kare hakkin dan Adam.

Yadda ake nuna rashin adalci a kasar, shi ma ya sa ta yi kokarin daukar matakai na son kai a duniya, ba tare da lura da bukatun sauran kasashe ba. Abubuwan da ya kamata wannan kasa ta koya daga kasashen Afirka, suna da yawa. (Bello Wang)

Afirka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Gwamnan Oyo Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Lawal Bayan Tsige shi

Gwamnan Oyo Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Lawal Bayan Tsige shi

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.