ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Abu Ya Sa Afirka Ta Zama Abin Koyi

by CMG Hausa
4 years ago
Afirka

Yau 18 ga watan Yuli rana ce da MDD ta kebe don tunawa da Nelson Mandela.

Idan an ba ni damar takaita ruhin marigayi Mandela da kalma daya, zan zabi “Hakuri”. Saboda ya taba bayyana cewa, “Lalata abu na da sauki, amma wanda ya dukufa wajen tabbatar da zaman lafiya shi ne jarumi.”

  • Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-3 Na Kasar Sin Ya Rabu Da Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

A sabili da ruhinsa na hakuri, bayan da Mandela ya kammala zamansa na shekaru 28 a gidan kurkuku, kuma ya zama shugaban kasa bakar fata na farko a tarihin kasar Afirka ta Kudu, bai nemi yin ramuwar gayya ga mutanen da suka taba cin zarafinsa ba.

ADVERTISEMENT

Don neman ganin an kafa wata sabuwar kasa, da samun sulhu tsakanin kabilu daban daban na kasar, ya nuna hakuri ga ‘yan kasarsa fararen fata, ta yadda a karshe dai ya cimma burin kare hakkin bakaken fata da kuma tabbatar da zaman daidaito a tsakaninsu da fararen fata.

A sauran kasashen Afirka ma, muna iya ganin yadda ra’ayi na hakuri ke taka muhimmiyar rawa. Misali a kasar Rwanda. Bayan abkuwar kisan kiyashi a shekarar 1994, wanda ya haddasa mutuwar mutane miliyan 1 a kasar, ba a ga wata ramuwar gayya daga ‘yan kabilar Tutsi ba. Maimakon haka, abun da aka yi shi ne neman samun maslaha. Cikin ‘yan kabilar Hutu dubu 120 da suka sa hannun kisan kiyashin, ban da yanke hukuncin kisa kan wasu mutane 90 da suka fi taka rawar aikata laifukan, sauran sun samu damar gyara halinsu. Hakurin da aka nuna ya tabbatar da kwanciyar hankali da hadin kan al’umma, inda wannan yanayi ya sa kasar kiyaye saurin karuwar tattalin arzinta na kashi 70% ko fiye da haka, tun bayan shekarar 2003.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Abin takaici shi ne, ra’ayi na hakuri da marigayi Mandela da sauran ‘yan Afirka ke da shi, har yanzu bai yi tasiri a wasu wurare ba, musamman ma babbar kasar da take daukar kanta a matsayin mai kare dimokuradiya da hakkin dan Adam.

A wannan kasa ra’ayin bambancin launin fata ya zama ruwa dare, inda yiwuwar ‘yan sanda su kama bakar fata ta ninka ta farar fata har sau 6. Kana an taba ganin yadda wani dan sanda ya danne wuyan wani saurayi bakar fata da gwiwa, har ya kashe shi, da yadda ‘yan sanda suka bindige wani bakar fata da ba shi da makami, wanda har aka samu raunukan bindigogi 60 a jikinsa, al’amuran da suka sanya al’ummar duniya cikin kaduwa.
Wannan kasa, ko da yake tana da karfi sosai a fannonin tattalin arziki da kimiyya da fasaha, amma tana ci gaba da fama da yanayi na koma baya, ta fuskar zaman daidaito a tsakanin al’umma, da kare hakkin dan Adam.

Yadda ake nuna rashin adalci a kasar, shi ma ya sa ta yi kokarin daukar matakai na son kai a duniya, ba tare da lura da bukatun sauran kasashe ba. Abubuwan da ya kamata wannan kasa ta koya daga kasashen Afirka, suna da yawa. (Bello Wang)

Afirka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Gwamnan Oyo Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Lawal Bayan Tsige shi

Gwamnan Oyo Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Lawal Bayan Tsige shi

LABARAI MASU NASABA

APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.