ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (3)

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Arewa

Ireti Heebah Kingibe

Arewa

Ireti Heebah Kingibe, injiniya ce yanzu kuma ‘yar siyasa ce, da ta lashe zaben kujerar Sanata mai wakiltar Babban Birnin Tarayya (FCT) a Majalisar Dattawan Nijeriya ta 10.

ADVERTISEMENT

An zabe ta a karkashin Jam’iyyar Labour a zaben ‘yan Majalisar Dattawa na 2023 kuma ita ce shugabar kwamitin majalisar dattawa kan harkokin mata. Kingibe ta fara aiki ne a matsayin injiniya mai kula da ingancin a Bradley Precast Concrete Inc a (1978-1979) sannan ta yi aiki da sashen zane-zanen sufuri na Minnesota har zuwa 1981.

Ta dawo Nijeriya don hidimar bautar kasa (NYSC) a 1981. Ta yi aiki a matsayin mai kula da ayyuka a sansanin sojojin saman Nijeriya da ke Ikeja, Legas. A shekarar 1982 ta shiga kamfanin ‘New Nigeria Construction Company’ da ke Kaduna a matsayin Injiniyar tsare-tsare kafin ta ci gaba da aikin tuntuba da kamfanin Belsam Limited a shekarar 1985. Daga 1990 zuwa 1994, ta kasance Injiniya na yankin Lodigiani Nigeria Limited, Legas, kuma yanzu ita ce mai ba da shawara sannan kuma babbar abokiyar hurda a Kelnic Associates a Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Sirrin Mallakar Miji 

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

Siyasar Kingibe ya fara ne a shekarar 1990 a matsayin mai ba da shawara ga shugaban rusasshiyar jam’iyyar Social Democratic Party (SDP). Ta tsaya takarar kujerar sanatan FCT a karkashin jam’iyyar ANPP a shekarar 2003, sannan ta koma jam’iyyar PDP a 2006. A 2014 ta koma APC, amma ta fice daga jam’iyyar a 2015 takarar Sanata.

A shekarar 2022, ta shiga jam’iyyar Labour, ta zama ‘yar takarar sanata a FCT a zaben 2023, kuma ta yi nasara. Kafin zaben, ta kaddamar da ainihin albashinta don gudanar da ayyukan samar da ababen more rayuwa a yankunan karkara a cikin Babban Birnin Tarayya Abuja.

Dr. Lydia Umar

Arewa

Dr. Lydia Umar Kwararriyar ce mai ilimi, ta kware wajen ci gaban al’umma , kuma mai fafutuka, wacce ta kware a fannin karatun (Social Studies). Ta kafa kungiyar wayar da kan jama’a ta Gender Awareness Trust (GAT) a jihar Kaduna a shekarar 2000, inda ta yi kokrin inganta daidaiton jinsi, kiwon lafiyar haihuwa, shigar mata a siyasance, da samar da zaman lafiya a tsakanin al’ummomin addinai daban-daban.

Tare da gogewa sama da shekaru 30 a aikin koyarwa da ayyukan ci gaba, Dokta Umar ta kasance mai himma wajen tafiyar da rikice-rikice, sasantawa, da gina zaman lafiya a matsayin mai koyarwa, sannan kuma mai bincike, kuma mai gudanarwa ta hukumomin gwamnati daban-daban da abokan ci gaban kasa da kasa.

Ta rike mukamai da dama da suka hada da mai bai wa kungiyar mata ta Afirka ta yamma shawara kan samar da zaman lafiya a yankin, da mamba a kungiyar raya zaman lafiya ta Afirka ta yamma (WANEP), ta yi mataimakiyar shugabar kungiyar sake fasalin ‘yan sanda a Nijeriya.

Dr. Umar ta wakilci Nijeriya a kungiyar Mata, daman lafiya da tsaro na Majalisar Dinkin Duniya kuma ta ba da gudummawa sosai ga shirye-shiryen zaman lafiya na yanki da na duniya.

Ayyukan da ta yi suna da yawa da suka hada da jagorantar kokarin bayar da shawarwari don amincewa da dokar hana cin zarafi (BAPP) a Jihar Kaduna a 2018 da kuma tuntubar ci gaba da tsare-tsare na hukumar zaman lafiya ta Kaduna.

Gudunmawar da Dakta Umar ta bayar wajen ’yancin mata da samar da zaman lafiya ya sanya ta zama jigo a fagen ci gaban gida da waje, an santa da jajircewarta na tabbatar da daidaiton jinsi da adalci a cikin al’umma.

Aisha Pamela Sadauki

Arewa

Aisha Pamela Sadauki ta kasance Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna a karkashin gwamnatin Soja Abubakar Tanko Ayuba. Ta rike mukamai da dama a cikin gwamnatin Jihar Kaduna, ciki har da kwamishiniyar ci gaban al’umma, matasa, da wasanni a 1988 da kwamishiniyar ilimi a 1989, kafin ta zama mataimakiyar gwamna daga 1990 zuwa 1992. gudummawar da ta bayar, ga jiha da kasa baki daya, Aisha Sadauki ta samu lambar yabo ta kasa (OON) a shekarar 2000.

Beni Butmak Lar

Arewa

Beni Lar, gogeggiyar ‘yan siyasa ce, sannan kuma masaniya ce a shari’a, kuma ‘yar majalisar wakilai mai wakiltar Langtang ta Arewa/Kudanci a Jihar Filato. Da farko an zabe ta a shekara ta 2007, tana yin wa’adi na biyar ne kuma ita ce shugabar kwamitin majalisar kan ‘yancin dan’Adam. Ita ce babbar ‘yar Solomon Lar, tsohon Gwamnan Jihar Filato, da Farfesa Mary Lar.

A duk tsawon aikinta na majalisa, Beni Lar ta kasance mai fafutukar kare hakkin mata, kare yara, da yancin dan’Adam. Ta yi yunkurin kare mutuncin cin zarafin yara, tallafawa shirye-shiryen yaki da fataucin mutane, da kafa hukumar kare yara da tilastawa yara ta kasa.

A shekara ta 2008, ta jagoranci kwamitin kula da harkokin mata na majalisar wakilai, kuma ta taka rawar gani wajen magance matsalolin da suka shafi jinsi, ciki har da bayar da shawarwarin shigar da mata cikin harkokin mulki da kuma kawar da nuna wariya ga mata.

Beni Lar ta yi addu’a kuma ta tofa albarkacin bakinta kan harkokin tsaro da ci gaban kasa. Ta jagoranci zanga-zangar nuna goyon bayanta ga kokarin da sojojin Nijeriya ke yi na ceto ‘yan matan makarantar Chibok da aka sace tare da yin kira da a inganta hanyoyin mota a mazabarta bayan hare-haren makiyaya. Ta ba da shawarar samar da wuraren kiwo ga fulani makiyaya tare da fafutukar samar da mafita mai dorewa ga Nijeriya a matsayinta na tsohuwar shugabar kwamitin kimiyya da fasaha ta majalisar.

Arewa
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Kafin Ki Nemi Saki, Nemi Amsar Waɗannan Tambayoyi Da Kanki
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?

MASU ALAKA

Sirrin Mallakar Miji 
Adon Gari

Sirrin Mallakar Miji 

January 25, 2026
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
Next Post
Karuwar Tattalin Arzikin Sin Na Sa Kaimi Ga Kamfanonin Duniya Da Su Hada Kansu Da Sin

Karuwar Tattalin Arzikin Sin Na Sa Kaimi Ga Kamfanonin Duniya Da Su Hada Kansu Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.