ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wike Ya Amince Da Kashe Naira Biliyan 8.4 Domin Shawo Kan Matsalar Tsaro A Abuja

by Sani Anwar
4 months ago
Wike

Hukumar kula da babban birnin tarayya Abuja, ta amince da kwangilar sama da naira biliyan 8.4, na ayyuka masu muhimmanci da suka haɗa da kwashe shara, samar da kayan tsaro da kuma bayar da tallafi ga waɗanda ambaliyar ruwa ta shafa.

An ɗauki matakin ne, yayin taron kwamitin zartarwa karo na 18, wanda ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya jagoranta a ranar Litinin, bayan kammala taron manema labarai.

  • HOTUNA: Wike Ya Buɗe Gidan Rediyo Don Yaƙin Neman Zaɓen Tinubu A Ribas
  • Wike Ya Amince Da Kashe Naira Biliyan 8.4 Domin Shawo Kan Matsalar Tsaro A Abuja

Shugaban hukumar kula da harkokin birnin tarayya Abuja (AMMC), Feliɗ Obuah, wanda ya yi wa ƴan jarida bayanin sakamakon, ya sanar da amincewa da wasu muhimman bayanai guda biyu.

ADVERTISEMENT

Na farko, in ji shi, wani muhimmin abu ne wanda zai taimaka wajen tsabtace yankin.

“A yau, mun gabatar da neman amincewa da wasu takardu guda biyu, waɗanda kwamitin ya amince da su.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

“Takardar farko, ita ce takardar neman amincewa da kwangilar kwashe shara a gundumomi huɗu na babban birnin tarayya da kuma samar da man dizal na AGO ga kamfanin kula da kwashe shara na Wupa, na tsawon shekara biyu. Adadin da aka bayar na waɗannan kwangiloli guda huɗu, ya kai kimanin naira biliyan 7.3,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, bayani na biyu, wanda kuma ya samu amincewar kwamitin shi ne, “neman amincewa da bayar da kwangilar sayan kayan abinci, domin tallafa wa waɗanda ambaliyar ruwa ta shafa a FCT.”

A wani gagarumin yunƙuri na ƙarfafa gine-ginen tsaro na babban birnin ƙasar, kwamitin ya kuma amince da sayo kayayyakin sadarwa na hukumar tsaro na babban birnin tarayya Abuja.

Musa Idris Onsachi, Daraktan kula da sayan kayayyaki na babban birnin tarayya, ya bayar da cikakken bayani a kan wannan amincewa, inda ya danganta ta kai tsaye da umarnin da ministan babban birnin tarayya ya bayar.

“A taron na kwamitin na yau, an amince da bayar da kwangilar sayan na’urorin sadarwa na gaggawa da sauran kayan aikin hukumar tsaro na FCT, a kan kuɗi naira 1,133,802,500 kacal,” in ji Mista Onsachi.

Ya jaddada wajibcin gudanar da aikin, inda ya bayyana cewa; “Dalilin wannan aikin shi ne, domin tallafa wa hukumar tsaro ta babban birnin tarayya Abuja, musamman wajen gudanar da ayyukansu a yankin.

Wike
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Masallata A Zamfara

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Masallata A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.