ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wike Ya Bukaci Bangarorin PDP Su Hada Kai Kafin Zaben 2027

by Sani Anwar
6 months ago
Wike

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Sakamakon gagarumin hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke, wanda ya kara ruruta rikicin jam’iyyar adawa ta PDP, ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya yi kira ga daukacin ‘ya’yan jam’iyyar, da su yi watsi da sabanin da ke tsakaninsu da kuma burinsu na sake gina jam’iyyar, gabanin babban zaben 2027.

Da yake magana da manema labarai a Abuja ranar Litinin, Wike ya bayyana hukuncin da kotun daukaka karar ta yanke na tabbatar da hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke na soke babban taron jam’iyyar na kasa na 2025, a matsayin wani babban abu mai ma’ana ga PDP.

  • Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’addan ISWAP 20 A Jihar Yobe
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 15, Sun Jikkata Da Dama A Katsina

Ya kuma bukaci bangarorin da ke rikici da juna da su kalli hukuncin ba a matsayin wani dalili na ci gaba da shari’a ba, a’a a matsayin wata dama ta sasantawa da sake sabunta jam’iyyar.

“A gare ni, dama ce ga kowa ya sake dawowa, don ganin yadda za mu iya ceto jam’iyyar. Amma ga shi za a fara zaben fidda gwani daga watan Afrilu, yanzu kuma ga shi muna watan Maris.

“Kowa ya bar son zuciyarsa, ka kuma bar abubuwan da kake so, ka dawo mu zauna mu sasanta, domin kuwa wannan dama ce muka sake samu,” in ji shi.

Ministan, wanda bangarensa ke takun-saka da wasu shugabannin jam’iyyar, kan yadda aka gudanar da babban taron da ake takaddama a kai, ya yi gargadin cewa; garzayawa zuwa kotun koli, ba zai bai wa jam’iyyar dama tare da taimakon ta ba, a zabe mai zuwa.

“Idan kun ce kuna son zuwa kotun koli, ku tuna za a yi zaben fidda gwani daga watan Afrilu zuwa na Mayu. Yanzu ku duba, a lokacin da kuka je kotun koli, kawai za ku cutar da kanku kawai, ku kuma cutar da jam’iyyar taku, wanda kuka ce kuna so kuma, wanda ba zai taimaka mana ba ne, “in ji shi.

Wike ya jaddada cewa, shigar kotun ya zama dole, domin batun shugabancin jam’iyyar ya wuce gona da iri, ta hanyar saba ka’idojin tsarin mulki da kuma dokokin zabe.

“Mutane da dama ba su fahimci inda matsalar take ba, ba batun shugabanci muke magana ba, idan kana maganar shugabanci, yanzu kana magana ne a kan harkokin cikin gida.

“Amma lokacin da kuka ce kuna karya kundin tsarin mulki, kuna karya dokar zabe, kuna karya ka’idojin hukumar zabe da kuma kundin tsarin mulkin jam’iyyarku, wannan ba ya cikin harkokin cikin gida na jam’iyya, dole ne kotu ta tsoma baki,” in ji shi.

Ministan babban birnin tarayya Abuja, ya bayyana gamsuwarsa da matakin da bangaren shari’a ya dauka, inda ya bayyana Juma’a a matsayin daya daga cikin ranakun farin ciki da ya samu a rayuwarsa.

Ya kara da cewa, “Dole ne a koda-yaushe, mu bi ka’ida, a matsayinmu na jam’iyyar adawa, bai kamata mu ki amincewa da hukuncin da aka yi ba.

Wike ya kuma yi amfani da damar wajen nuna mahimmancin jam’iyyar PDP a matsayin dandalin adawa na farko na kasar, inda ya bayyana sauran kananan jam’iyyu da cewa, ba su da wani tasiri.

Da yake yin karin haske kan makomar shugabancin jam’iyyar, Wike ya bayyana cewa; kwamitin riko na jam’iyyar PDP, wanda aka kafa bayan karewar wa’adin jami’an da suka gabata, sun ne halastattun shugabannin da aka sani.

Ya sanar da cewa, tuni kwamitin ya samu amincewar gudanar da sabon babban taron kasa a ranakun 29 da 30 ga watan Maris.

Wike
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Next Post
Yadda ‘Yan Boko Haram Suka Kashe Kwamandojin Soja 3 A Mako Daya

Yadda ‘Yan Boko Haram Suka Kashe Kwamandojin Soja 3 A Mako Daya

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.