ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wike Ya Bukaci Bangarorin PDP Su Hada Kai Kafin Zaben 2027

by Sani Anwar
3 months ago
Wike

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sakamakon gagarumin hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke, wanda ya kara ruruta rikicin jam’iyyar adawa ta PDP, ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya yi kira ga daukacin ‘ya’yan jam’iyyar, da su yi watsi da sabanin da ke tsakaninsu da kuma burinsu na sake gina jam’iyyar, gabanin babban zaben 2027.

Da yake magana da manema labarai a Abuja ranar Litinin, Wike ya bayyana hukuncin da kotun daukaka karar ta yanke na tabbatar da hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke na soke babban taron jam’iyyar na kasa na 2025, a matsayin wani babban abu mai ma’ana ga PDP.

  • Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’addan ISWAP 20 A Jihar Yobe
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 15, Sun Jikkata Da Dama A Katsina

Ya kuma bukaci bangarorin da ke rikici da juna da su kalli hukuncin ba a matsayin wani dalili na ci gaba da shari’a ba, a’a a matsayin wata dama ta sasantawa da sake sabunta jam’iyyar.

“A gare ni, dama ce ga kowa ya sake dawowa, don ganin yadda za mu iya ceto jam’iyyar. Amma ga shi za a fara zaben fidda gwani daga watan Afrilu, yanzu kuma ga shi muna watan Maris.

“Kowa ya bar son zuciyarsa, ka kuma bar abubuwan da kake so, ka dawo mu zauna mu sasanta, domin kuwa wannan dama ce muka sake samu,” in ji shi.

Ministan, wanda bangarensa ke takun-saka da wasu shugabannin jam’iyyar, kan yadda aka gudanar da babban taron da ake takaddama a kai, ya yi gargadin cewa; garzayawa zuwa kotun koli, ba zai bai wa jam’iyyar dama tare da taimakon ta ba, a zabe mai zuwa.

“Idan kun ce kuna son zuwa kotun koli, ku tuna za a yi zaben fidda gwani daga watan Afrilu zuwa na Mayu. Yanzu ku duba, a lokacin da kuka je kotun koli, kawai za ku cutar da kanku kawai, ku kuma cutar da jam’iyyar taku, wanda kuka ce kuna so kuma, wanda ba zai taimaka mana ba ne, “in ji shi.

Wike ya jaddada cewa, shigar kotun ya zama dole, domin batun shugabancin jam’iyyar ya wuce gona da iri, ta hanyar saba ka’idojin tsarin mulki da kuma dokokin zabe.

“Mutane da dama ba su fahimci inda matsalar take ba, ba batun shugabanci muke magana ba, idan kana maganar shugabanci, yanzu kana magana ne a kan harkokin cikin gida.

“Amma lokacin da kuka ce kuna karya kundin tsarin mulki, kuna karya dokar zabe, kuna karya ka’idojin hukumar zabe da kuma kundin tsarin mulkin jam’iyyarku, wannan ba ya cikin harkokin cikin gida na jam’iyya, dole ne kotu ta tsoma baki,” in ji shi.

Ministan babban birnin tarayya Abuja, ya bayyana gamsuwarsa da matakin da bangaren shari’a ya dauka, inda ya bayyana Juma’a a matsayin daya daga cikin ranakun farin ciki da ya samu a rayuwarsa.

Ya kara da cewa, “Dole ne a koda-yaushe, mu bi ka’ida, a matsayinmu na jam’iyyar adawa, bai kamata mu ki amincewa da hukuncin da aka yi ba.

Wike ya kuma yi amfani da damar wajen nuna mahimmancin jam’iyyar PDP a matsayin dandalin adawa na farko na kasar, inda ya bayyana sauran kananan jam’iyyu da cewa, ba su da wani tasiri.

Da yake yin karin haske kan makomar shugabancin jam’iyyar, Wike ya bayyana cewa; kwamitin riko na jam’iyyar PDP, wanda aka kafa bayan karewar wa’adin jami’an da suka gabata, sun ne halastattun shugabannin da aka sani.

Ya sanar da cewa, tuni kwamitin ya samu amincewar gudanar da sabon babban taron kasa a ranakun 29 da 30 ga watan Maris.

Wike
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tinubu Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Kan Jajircewarsu Wajen Kawo Karshen Ta’addanci
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Yadda ‘Yan Boko Haram Suka Kashe Kwamandojin Soja 3 A Mako Daya

Yadda ‘Yan Boko Haram Suka Kashe Kwamandojin Soja 3 A Mako Daya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.