Ministan Abuja Nyesom Wike ya bada umarnin gaggawa na rushe duk wani wuri da ake zargin maɓoyar masu laifi ce a gundumar Karmajiji da ke yankin Kukwaba a Abuja, inda ya bayyana wurare a matsayin inda masu aikata laifin ke ɓoyewa a babban birnin tarayya.
Ministan ya bada wannan umarni ne a makon da ya gabata a lokacin da ya kai ziyara a wasu wuraren zama ba bisa ƙa’ida ba tare da rakiyar jami’an tsaro jim kaɗan bayan kammala taron kwamitin tsaro a ƙoƙarin sa na karfafa tsaro a birnin tarayya Abuja
A cewar sa, bayanan sirri sun gano wasu wurare da ake zargin sun zama maɓoya ga masu aikata laifuffuka bayan kai wasu hare-hare a wurare daban-daban a Abuja
Ya kuma bayyana irin waɗannan wurare a matsayin babbar barazanar tsaro, sai dai ya ce a ƙarƙashin kulawarsa irin waɗannan wurare ba za su taɓa sha ba, zai kauda su.
“Duba wannan wuri, ba zaka iya sanin wa yake zama ba, ta ya ya zamu iya gano su? Ta ina zamu gano inda suke? yanzu wannan daidai ne a cikin birnin irin Abuja? Wannan tamkar muna kan wata nakiya ce, ta inda babu wata hanya da zamu kyale wannan abu ya cigaba da faruwa. Shugabancin birnin tarayya Abuja ba zai taɓa kyale masu laifi su zauna lafiya ba” inji shi
Haka kuma ministan ya baiwa ɓangaren lura da cigaba umarni da ya gaggauta rushe duk wani gini da aka yi ba bisa ƙa’ida ba sannan su yi aikin tare kwamishinan ƴan sanda na birnin tarayya Abuja, Ahmad Sunusi tare da sauran hukumomin tsaro
Ya ce wannan aikin na daga cikin abubuwan da shugabancin da ya sanya gaba, na kauda duk wata barazanar tsaro tare da maido da zaman lafiya da aminci a cikin birnin tarayya Abuja.
Kazalika minista Wike ya yi gargaɗi jama’ar da ke bada wurare ana amfani da gine-gine ba bisa ƙa’ida ba, zai sanya ƙafar wando ɗaya da su kamar yadda doka ta tanada.
Ya kuma ƙara tabbatar da jajircewar shugabancin sa na cigaba da lura da sa ido akan sha’anin tsaro a faɗin abuja tare da kare rayuka da dukiyoyi a matsayin abu mai mahimmanci da ya sanya gaba
Nyesom Wike ya ce shugabancin sa zai cigaba da gano irin waɗannan wurare tare da rushe su domin kauda barazanar tsaro a zukatan al’umma, ta hanyar aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro domin a tabbatar Abuja ta samu tsaro da amince ga al’ummar da ke zaune a cikin ta












