Yau Litinin, shugaban Sin Xi Jinping ya tattauna da yarima mai jiran gado kuma firaministan kasar Saudiyya Mohammed bin Salman ta wayar tarho bisa bukatar yariman.
Dangane da halin da ake ciki a Gabas ta Tsakiya da yankin Gulf, Xi Jinping ya jaddada cewa Sin na goyon bayan tsagaita bude wuta nan take, kuma tana goyon bayan duk wani kokari da zai taimaka wajen maido da zaman lafiya, tare da bin ka’idar warware rikici ta hanyar siyasa da diflomasiyya.
Ya ce ya kamata a kiyaye zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigin tekun Hormuz yadda ya kamata, wanda ya dace da muradun kasashen yankin da kuma al’ummar duniya.
Ban da haka kuma, Sin na goyon bayan kasashen yankin su gina yankin ta yadda za a samu zaman lafiya tsakanin makwabta, kana mai ci gaba da tsaro da kuma hadin gwiwa.A nasa bangare, Mohammed Bin Salman ya bayyana cewa, Sin babbar kasa ce mai daukar alhaki a duniya kuma kullum tana tsayawa tsayin daka kan matsayin adalci.
Ya ce kasar Saudiyya na son karfafa tuntubar juna da hadin gwiwa da Sin don kiyaye yanayin tsagaita bude wuta da kuma tabbatar da tsaro da ’yancin zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigin tekun Hormuz.(Safiyah Ma)















Discussion about this post