Sakatare janar na JKS Xi Jinping, ya yi kira da a inganta karfin jam’iyyar na jagorantar kanta bisa nagarta da matakai masu inganci.
Xi Jinping wanda kuma shi ne shugaban kasar kuma shugaban hukumar koli mai kula da harkokin soji, ya bayyana haka ne yau Litinin yayin taro na 5 na hukumar koli mai sa ido kan tabbatar da da’a ta JKS, da aka yi a birnin Beijing.
Shugaba Xi ya kuma bukaci kada a wuce gona da iri wajen amfani da karfin iko, haka kuma a kara kaimi a yaki da cin hanci bisa fahimta da jajircewa, ta yadda za a samar da tabbaci mai karfi na cimma burika da ayyukan dake kunshe cikin shirin raya kasa na shekaru biyar biyar, daga shekarar 2026 zuwa ta 2030. (FMM)















Discussion about this post