Tawagar ƙwallon ƙafa ta Morocco na fuskantar damuwa gabanin wasanta na farko a Gasar Kofin Duniya ta 2026 da Brazil, bayan da manyan ‘yan wasanta biyu, Abdessamad Ezzalzouli da Noussair Mazraoui, suka samu raunuka a wasan sada zumunta da Norway.
Ezzalzouli ya samu raunin ƙafa wanda ya hana shi dawowa buga zagaye na biyu, yayin da Mazraoui ya bar fili bayan mintuna 29 kacal sakamakon raunin kafaɗa. Wasan dai ya kare ne da ci 1-1 bayan Morocco ta fara jefa ƙwallo kafin Norway ta rama.
Kocin Morocco, Mohamed Ouahbi, ya ce duk da kyakkyawan rawar da tawagarsa ta taka a wasan, raunukan da ‘yan wasan biyu suka samu ne babban abin damuwarsa a halin yanzu. Ya ce har yanzu ba a tabbatar da tsananin raunukan ba.
Morocco za ta fara yaƙin neman yin fice a rukunin D ne da karawa da Brazil a filin wasa na MetLife Stadium ranar Lahadi, inda take fatan maimaita bajintar da ta yi a gasar da ta gabata lokacin da ta kai wasan kusa da na ƙarshe.















Discussion about this post