ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

by Sulaiman
3 weeks ago
Imam

Kashim Ibrahim Imam, fitaccen dan siyasa kuma abokin kasuwancin Shugaba Bola Tinubu, ya shiga sahun ’yan adawar da ke neman kifar da gwamnatin shugaban kasa daga mulki a babban zaɓen shekarar 2027.

A cewarsa da kansa, Imam ya yanke shawarar kawo karshen shekaru 36 na abota tsakaninsa da Shugaba Tinubu domin mara wa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, baya a takarar shugaban kasa ta shekara mai zuwa.

Babu wani rahoto da ya nuna cewa akwai saɓani na siyasa ko kasuwanci tsakanin Shugaba Tinubu da Kashim Imam.Abin da aka sani kawai shi ne wani ɗan gajeren rahoto da dan siyasar na Borno ya wallafa a shafinsa na sada zumunta watanni da suka gabata, inda ya yi watsi da goyon bayansa ga Tinubu saboda abin da ya kira “rashin adalci”, tare da cewa akwai “ɗimbin arziki a Nijeriya, na ɓoye ko na fili.”

ADVERTISEMENT

Rahotannin kafafen yada labarai da bayanan fadar shugaban kasa sun nuna cewa Tinubu da Imam na ci gaba da kyakkyawar alaka har zuwa farkon wannan gwamnati.Watanni biyar bayan shugaban kasa ya hau mulki, ya yi wani naɗin muƙami da ya yi, ya haifar da cece-kuce a tsakanin jama’a.

Imam Kashim Imam, matashi mai shekaru 24 da ya kammala karatun injiniyanci kuma dan wani abokin siyasar shugaban kasa, an nada shi shugaban hukumar kula da gyaran hanyoyi ta tarayya (FERMA), sanadiyyar wannan naɗin ne ya haifar da cece-kuce tsakanin jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

Kafafen yada labarai sun ruwaito cewa mahaifinsa, Kashim Ibrahim Imam, ya taka muhimmiyar rawa sosai wajen yakin neman zaben Tinubu da kuma nasararsa a zaben shugaban kasa.

Nadin na daya daga cikin na farko da shugaban kasa ya yi, duk da cewa ya dauki kusan watanni uku kafin ya nada ministoci 45 da suka shiga majalisar ministocinsa.

Har watanni 12 kafin karewar zangon mulkinsa na farko, mukaman jakadun Nijeriya da dama ba a cike su ba. Wannan ya nuna irin muhimmancin da Tinubu ya bai wa nadin matashin Imam a matsayin shugaban FERMA da kuma irin kusancin da ya sa aka yi la’akari da shi a watan Oktoban 2023.Sai dai, cece-kucen da jama’a suka yi, ya yi tasiri sosai har shugaban kasa ya janye nadin bayan mako guda.

Baban Imam, wanda ya taba kasancewa babban abokin hamayyar Ali Modu Sheriff a siyasar Borno kuma ya yi takara sau biyu da tsohon gwamnan, ya kasance daya daga cikin jiga-jigan taron jam’iyyun adawa da aka gudanar a Ibadan, jihar Oyo, a karshen watan Afrilu.

Jam’iyyun siyasar sun nemi samar da hadin kai tare da tsayar da dan takarar shugaban kasa guda daya domin kalubalantar Shugaba Tinubu a watan Janairu mai zuwa, har ma suka fitar da sanarwar hadin kai.

Sai dai hadakar ta watse bayan mako guda bayan tsohon gwamnan Anambra, Peter Obi, da tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, sun fice daga jam’iyyar ADC zuwa NDC domin tsayawa takara tare a karkashin tikiti guda.

Imam
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao
  • Sulaiman
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai
Rahotonni

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Noma
Rahotonni

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Next Post
Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi

An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi

June 29, 2026
Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

June 29, 2026
Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

June 28, 2026
Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.