ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Kashim Imam Ke Yi A Yanzu?

by Sulaiman
1 month ago
Imam

Kashim Ibrahim Imam, fitaccen dan siyasa kuma abokin kasuwancin Shugaba Bola Tinubu, ya shiga sahun ’yan adawar da ke neman kifar da gwamnatin shugaban kasa daga mulki a babban zaɓen shekarar 2027.

A cewarsa da kansa, Imam ya yanke shawarar kawo karshen shekaru 36 na abota tsakaninsa da Shugaba Tinubu domin mara wa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, baya a takarar shugaban kasa ta shekara mai zuwa.

Babu wani rahoto da ya nuna cewa akwai saɓani na siyasa ko kasuwanci tsakanin Shugaba Tinubu da Kashim Imam.Abin da aka sani kawai shi ne wani ɗan gajeren rahoto da dan siyasar na Borno ya wallafa a shafinsa na sada zumunta watanni da suka gabata, inda ya yi watsi da goyon bayansa ga Tinubu saboda abin da ya kira “rashin adalci”, tare da cewa akwai “ɗimbin arziki a Nijeriya, na ɓoye ko na fili.”

ADVERTISEMENT

Rahotannin kafafen yada labarai da bayanan fadar shugaban kasa sun nuna cewa Tinubu da Imam na ci gaba da kyakkyawar alaka har zuwa farkon wannan gwamnati.Watanni biyar bayan shugaban kasa ya hau mulki, ya yi wani naɗin muƙami da ya yi, ya haifar da cece-kuce a tsakanin jama’a.

Imam Kashim Imam, matashi mai shekaru 24 da ya kammala karatun injiniyanci kuma dan wani abokin siyasar shugaban kasa, an nada shi shugaban hukumar kula da gyaran hanyoyi ta tarayya (FERMA), sanadiyyar wannan naɗin ne ya haifar da cece-kuce tsakanin jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Kafafen yada labarai sun ruwaito cewa mahaifinsa, Kashim Ibrahim Imam, ya taka muhimmiyar rawa sosai wajen yakin neman zaben Tinubu da kuma nasararsa a zaben shugaban kasa.

Nadin na daya daga cikin na farko da shugaban kasa ya yi, duk da cewa ya dauki kusan watanni uku kafin ya nada ministoci 45 da suka shiga majalisar ministocinsa.

Har watanni 12 kafin karewar zangon mulkinsa na farko, mukaman jakadun Nijeriya da dama ba a cike su ba. Wannan ya nuna irin muhimmancin da Tinubu ya bai wa nadin matashin Imam a matsayin shugaban FERMA da kuma irin kusancin da ya sa aka yi la’akari da shi a watan Oktoban 2023.Sai dai, cece-kucen da jama’a suka yi, ya yi tasiri sosai har shugaban kasa ya janye nadin bayan mako guda.

Baban Imam, wanda ya taba kasancewa babban abokin hamayyar Ali Modu Sheriff a siyasar Borno kuma ya yi takara sau biyu da tsohon gwamnan, ya kasance daya daga cikin jiga-jigan taron jam’iyyun adawa da aka gudanar a Ibadan, jihar Oyo, a karshen watan Afrilu.

Jam’iyyun siyasar sun nemi samar da hadin kai tare da tsayar da dan takarar shugaban kasa guda daya domin kalubalantar Shugaba Tinubu a watan Janairu mai zuwa, har ma suka fitar da sanarwar hadin kai.

Sai dai hadakar ta watse bayan mako guda bayan tsohon gwamnan Anambra, Peter Obi, da tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, sun fice daga jam’iyyar ADC zuwa NDC domin tsayawa takara tare a karkashin tikiti guda.

Imam
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya
  • Sulaiman
    An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai
  • Sulaiman
    Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel
  • Sulaiman
    Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

MASU ALAKA

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
Rahotonni

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu
Rahotonni

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
Rahotonni

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Next Post
Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
Imam

Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure

July 19, 2026
An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026
Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

July 18, 2026
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

July 18, 2026
Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

July 18, 2026
Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

July 18, 2026
Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

July 18, 2026
Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

July 18, 2026
Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.