Kashim Ibrahim Imam, fitaccen dan siyasa kuma abokin kasuwancin Shugaba Bola Tinubu, ya shiga sahun ’yan adawar da ke neman kifar da gwamnatin shugaban kasa daga mulki a babban zaɓen shekarar 2027.
A cewarsa da kansa, Imam ya yanke shawarar kawo karshen shekaru 36 na abota tsakaninsa da Shugaba Tinubu domin mara wa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, baya a takarar shugaban kasa ta shekara mai zuwa.
Babu wani rahoto da ya nuna cewa akwai saɓani na siyasa ko kasuwanci tsakanin Shugaba Tinubu da Kashim Imam.Abin da aka sani kawai shi ne wani ɗan gajeren rahoto da dan siyasar na Borno ya wallafa a shafinsa na sada zumunta watanni da suka gabata, inda ya yi watsi da goyon bayansa ga Tinubu saboda abin da ya kira “rashin adalci”, tare da cewa akwai “ɗimbin arziki a Nijeriya, na ɓoye ko na fili.”
Rahotannin kafafen yada labarai da bayanan fadar shugaban kasa sun nuna cewa Tinubu da Imam na ci gaba da kyakkyawar alaka har zuwa farkon wannan gwamnati.Watanni biyar bayan shugaban kasa ya hau mulki, ya yi wani naɗin muƙami da ya yi, ya haifar da cece-kuce a tsakanin jama’a.
Imam Kashim Imam, matashi mai shekaru 24 da ya kammala karatun injiniyanci kuma dan wani abokin siyasar shugaban kasa, an nada shi shugaban hukumar kula da gyaran hanyoyi ta tarayya (FERMA), sanadiyyar wannan naɗin ne ya haifar da cece-kuce tsakanin jama’a.
Kafafen yada labarai sun ruwaito cewa mahaifinsa, Kashim Ibrahim Imam, ya taka muhimmiyar rawa sosai wajen yakin neman zaben Tinubu da kuma nasararsa a zaben shugaban kasa.
Nadin na daya daga cikin na farko da shugaban kasa ya yi, duk da cewa ya dauki kusan watanni uku kafin ya nada ministoci 45 da suka shiga majalisar ministocinsa.
Har watanni 12 kafin karewar zangon mulkinsa na farko, mukaman jakadun Nijeriya da dama ba a cike su ba. Wannan ya nuna irin muhimmancin da Tinubu ya bai wa nadin matashin Imam a matsayin shugaban FERMA da kuma irin kusancin da ya sa aka yi la’akari da shi a watan Oktoban 2023.Sai dai, cece-kucen da jama’a suka yi, ya yi tasiri sosai har shugaban kasa ya janye nadin bayan mako guda.
Baban Imam, wanda ya taba kasancewa babban abokin hamayyar Ali Modu Sheriff a siyasar Borno kuma ya yi takara sau biyu da tsohon gwamnan, ya kasance daya daga cikin jiga-jigan taron jam’iyyun adawa da aka gudanar a Ibadan, jihar Oyo, a karshen watan Afrilu.
Jam’iyyun siyasar sun nemi samar da hadin kai tare da tsayar da dan takarar shugaban kasa guda daya domin kalubalantar Shugaba Tinubu a watan Janairu mai zuwa, har ma suka fitar da sanarwar hadin kai.
Sai dai hadakar ta watse bayan mako guda bayan tsohon gwamnan Anambra, Peter Obi, da tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, sun fice daga jam’iyyar ADC zuwa NDC domin tsayawa takara tare a karkashin tikiti guda.














Discussion about this post