ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
1 year ago
Aisha Tafida Gombe

Kamar yadda shafin RUMBUN NISHADI ya saba zakulo muku fitattun jaruman finafinan hausa har ma da masu tasowa, kana da labaru na musamman wadanda suka shafin cikin masana’ar kannywood, a yau ma shafin na tafe da wata jarumar da ake damawa da ita a yanzu wato AISHA TAFIDA EL-NAFATY wacce aka fi sani da AISHA TAFIDA GOMBE. Inda ta bayyanawa masu karatu takaitaccen tarihinta har ma da wasu batutuwan da suka shafi sana’arta ta fim.

Ga dai tattaunawar tare da wakiliyar mu RABI’AT SIDI BALA Kamar haka: Da farko masu karatu za su so su ji cikakken sunanki.

Sunana Aisha Tafida El-Nafaty wacce aka fi kira da Aisha Tafida Gombe.

ADVERTISEMENT

 

Ko za ki fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

Ni dai haifaffiyar garin Gombe ce, nayi makarantar firamare da sakandre a “Gobernment Girls Secondary School” dake cikin garin Gombe, daga nan kuma sai na dawo Kano da zama na fara sana’ar fim.

 

Ya batun ci gaba da karatu akwai ra’ayin hakan a nan gaba ko babu?

Ina da burin hakan in sha Allah idan Allah ya amince.

 

Ya batun aure shin kin taba yi ko kuwa tukunna dai?

Na taba yin Aure inada yara 3.

 

Me ya ja hankalin ki har ki ka tsunduma harkar fim?

Kawai ra’ayi ne, saboda tun ina karama fim yana burge ni sai nake ji a raina kamar idan na girma ni ma zan iya yi, sai kuma Allah ya amince.

 

Ya gwagwarmayar shiga cikin masana’antar ta kasance?

To ni dai gaskiya ban sha wata wahala sosai ba wajen shiga fim, sai dai kalubale kawai dana samu da iyaye da ‘yan’uwa su ma daga baya sun amince kuma sun bani goyon baya sosai.

 

Za ki yi kamar shekara nawa da fara fim?

Shekata biyu kawai nayi ina fim dana samu miji sai nayi aure, da auren ya kare ne sai kuma na sake dawo wa fim din saboda ita ce sana’ar dana iya nake yi.

Idan na fahimce ki kina so ki ce a can baya kin taba yin fim, yanzu dawowa ki ka yi kenan, to a wacce shekara ki ka fara a wancen lokacin, kuma a wacce shekara ki ka dawo yanzu din?

Eh! haka ne, na gama sakandare dina a ‘G.G.C Doma’ dake garin Gombe a shekarar 2011, sai na shiga harkar fim 2013 kuma nayi aure, 2023 Kuma da auren ya kare sai na dawo sana’ata.

 

Da wane fim ki ka fara a wancen lokacin da kuma wannan lokacin da ki ka dawo?

A wancan lokacin na fara fim din ‘Wa Zai Auri Jahila’ da kuma ‘Kallo Ya Koma Sama’ na ‘Alkausar Mobies’, fim din Darakto Ibrahim Bala. Bayan na dawo kuma fim din dana fara shiga na Abubakar Bashir Meshadda ‘Ana Dara Ga Dare’ da ‘Halimatussdiyya’ da kuma ‘Hauwa kulu’.

 

Wane rawa ki ka taka cikin wadannan finafinan, shin ke ki ka ja ragamar shirin matsayin jaruma/tauraruwa cikin shirin ko ya abun ya kasance?

‘Wazai Auri Jahila’ na fito ne a matsayin jahila amma a fim din, wacce ba ta yi karatun addini ba, bata san yadda za ta bautawa Allah ba, wanda ko suratul fatiha bata iya karantawa ba, amma dai ta yi ilimin boko sosai sakamakon mahaifinta attajiri ne a kasar waje ma tayi karatun.

‘Kallo Ya Koma Sama’ na taso cikin maraici na rashin uwa, na rayu hannun kishiyar uwa, ta wahalar da ni sosai, amma ta nunawa ‘yar ta gata ta kyale yarinyar tana yin abin da take so wanda a karshe ta lalace ni kuma na zama mutumiyar kirki.

‘Halimatussadiyya’ kuma mu biyu ‘Ya’ya mata mahaifinmu ya Haifa (Yakubu Muhd) kuma yanada burin mu gaji sana’ar sa na tuki sai dai mata wanda a karshe dai ya aurar da ni ita kuma kanwata (Hassana Muh’d) burinta ta shiga fim ta zama ‘yar wasan hausa, ta cinma burinta amma babanmu yayi fushi da ita.

Eh! ni na taka rawa amma a sauran rol aka bani.

 

Kin yi finafinai sun kai kamar guda nawa?

A kalla dai guda 10 ko 15 haka.

 

Wane fim ki ka fi so cikin finafinan da ki ka fito, wanne ne kuma idan ki ka tuna shi ki ke da-kin-sanin yinsa, kuma me ya sa?

Na fi son fim din ‘Wa Zai Auri Jahila’ saboda da shi na fara, amma gaskiya duk fim din dana yi babu wanda nake da-na-sanin fitowa a cikinsa, saboda tun kafin nayi sai an bani labarin na karanta na ga rol din da zan yi tukuna.

 

Ko akwai wani kalubale da ki ka taba fuskanta bayan shigar ki cikin masana’antar a wancen lokacin har ma da wannan lokacin?

Gaskiya Alhamdulillah! ban taba samun kowanne kalubale ba, kuma na zauna da kowa lafiya ban samu abokin fada ba.

 

Wane irin nasarori ki ka samu sanadiyyar harkar fim?

Gaskiya ba za su kirgu ba, na samu nasarori masu tarin yawa wanda har yanzu a cikinsa nake.

 

Ko akwai wani abu daya taba saka ki cikin farin ciki ko akasin haka sanadiyyar fim, wanda ba za ki taba iya mantawa da shi ba?

Farin cikina daya a rayuwata da Allah ya sa aka haife ni a cikin musulunci al’ummar Annabi Muhammad (S.A.W) Alhamdulillah. Ranar damuwata kuma shi ne ranar da mahaifiyata ta rasu amma Alhamdulillah tayi kyakyakyawar mutuwa da muke kyautata mata zaton rahamar Allah ta rasu cikin azumi a goman karshe ranar juma’a kuma ta rasu ne sakamakon haihuwa gawarta tana murmushi kamar za ka yi magana ta amsa, Allah ya ji kan dukkan magabatanmu ya sa mu cika da kyau da imani idan tamu ta zo.

 

Ya mu’amularki take da kawayenki wadanda ku ke tare tun kafin ki fara fim, musamman a yanzu da ki ka zama jaruma?

Mu’amalar mu bata canza ba gaskiya, muna nan kamar yadda muke da su a baya.

 

Mene ne burinki na gaba gake da fim?

Ba ni da wani buri a fim kuma, tunda gani a cikinta ina yi a matsayin sana’a.

 

Wane jarumi ko jaruma ce ke burge ki tun kafin ki fara fim?

Jarumaina kafin na shiga fim Mansura Isah, Farida Jalal da kuma Ahmad S. Nuhu Allah ya ji kansa da rahama.

 

Ko akwai jaruman da ki ke sha’awar yin fim tare da su?

Ai gaskiya kusan duka nayi aiki da su, kuma ni duk wanda aka hada ni aiki da shi za mu yi bana zabe.

 

Bayan fim kina wata sana’ar ne?

Eh, ina sana’ar sayar da kayayyakin mata haka, atamfa, lesis, abaya takalma, shadda, da dai sauransu.

 

A gida ki ke siyarwa ko kina da wani waje na daban da ake zuwa a siya a can kamar shago da sauransu?

A gida ne, kuma na kan saya na turawa kanne na da kawayena ma duka, su sayar su ma su samu wani abu.

 

Ya batun soyayya ko akwai wani cikin masana’antar daya taba nuna cewa yana sonki zai aure ki?

A’a bana soyayya da kowa a cikin masana’antar gaskiya.

 

Yaushe ki ke saka ran kara yin aure?

Gaskiya tukuna babu wannan zancen a raina yanzu, Alhamdulillah tunda nayi auren har inada yara, Allah ya rayasu da imani., amma ba wai na ce ba zan sake yi ba, babu dai tunanin sakewar a kusa gaskiya.

 

Wacce shawara za ki bawa sauran abokanan sana’arki na fim har ma da masu kokarin shiga cikin masana’antar?

Shawarar da zan basu musamman mata a rike mutuncin kai, a dinga tuna rayuwar duniyar nan kalilance, aji tsoron Allah, a dinga tuna mutuwa kowani lokaci, kuma a dauki fim a matsayin sana’a an fi ganin Albarkar ta.

 

Ko kinada wadanda za ki gaisar?

Gaisuwa ga dukkan masoyana da kuma ‘yan’uwa musulmi gabadaya na gode.

 

Muna godiya ki huta lafiya

Ni ma na gode.

Aisha Tafida Gombe
Rabilu Sanusi Bena
+ posts Bio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Barcelona Ta Kammala Daukar Anthony Gordon Daga Newcastle
Aisha Tafida Gombe
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Nishadi

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

May 23, 2026
Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano
Nishadi

Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano

May 16, 2026
Next Post
Maniyyata Daga Turai Akan Dawakai Sun Isa Kasar Saudiyya Domin Yin Aikin Hajjin 2025

Maniyyata Daga Turai Akan Dawakai Sun Isa Kasar Saudiyya Domin Yin Aikin Hajjin 2025

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.