ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Alkur’ani Ya Dace Da Kimiyya Da Fasahar Karni Na 21

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani and Sulaiman
2 months ago
Alkur'ani

Alhamdulillahi… kamar yadda duk musulmai suka yi imani cewa, littafin Alkur’ani mai girma, wanda ubangiji tabaraka wata’ala ya saukarwa masoyinsa, kuma fiyayyen halitta, Annabi Muhammad SAW, ya zama gagara-badau, don haka, ya gagari duk masana, ta yadda suka gaza kai karshen ilimin da ke tattare acikinsa.

Duk nisan zamani da sauyinsa, za kaga Alkur’ani ya tattaro ilimin wannan zamanin. Don haka, ubangiji ke horo da cewa, “a zurfafa bincike acikinsa”, a wani wuri kuma cewa, “ka ce, ya ubangiji kara min ilimi”.

  • Shin Bunkasar Sabbin Fasahohi Na Iya Illata Walwalar Jama’a?
  • Ista: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Juma’a Da Litinin A Matsayin Ranakun Hutu

A wannan makon, shafin namu mai albarka, tsakuro mana wani abu ya yi na ilimi daga Tafsirin bana, wanda yayi daidai da fahimtar wannan karni mai cike da kimiyya da fasaha.

ADVERTISEMENT

 

Ga wasu da muka tsakuro muku:

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

Kasa Na Samun Daukaka Ne Da Mutunta Dukkan Al’umma

Shehu Isma’ila Umar Almadda (Mai Diwani), ya cigaba da bayani akan banbancin garuruwa biyu mabanbanta – Birni da Kauye, inda ya ce, Birni yana samun cigaba sabida tsarinsa na sassauyawa duba da yadda Baƙi ke sauka acikinsa amma Kauye, wata rana nemansa ake a rasa sabida tsarinsa na tsayawa kan tsari daya da kin amsar baki.

Birni, ya kan bayar da ‘yancin cakuduwar al’adu, da tsarin sanya tufafi, inda kowace al’ada za ta saka kayan al’adunta kuma wata al’umma ta koyi wani abu daga cikin al’adun wata al’umma da suke cakude a wurin zama daya.

Har ila yau, Birni yana bayar da ‘yancin yin addini, ‘yancin yare, inda Shehin ya yi kira da cewa, a kula da dora Larabci akan sauran Yarurruka, kowane Yare, zai iya zama yaren addini.

‘Yancin siyasa, ‘yancin kasuwanci, ‘yancin kula da lafiyar tsoffi da kananan yara, duk birni ya tanadi wannan.

Akwai ‘yancin tambaya ta hankali wadda zata kawo cigaba ko fadan ra’ayi, duk a tsarin Birni, inda ya kafa misali da cewa, wasu sunce, “da ba a soki tafiyar sufaye ba, da wasu littattafan da ilimi basu samu ba”, haka zalika gun siyasa, “ba don ‘yancin fadan ra’ayi ba, da sukar gwamnati a inda ta gaza, da wasu cigaban ba a same su ba”, don haka, duk kasar da ta bayar da wadannan ‘yancin, ita ta gasgata Allah, don ta yarda komai ba daya ba ne, Allah shi kadai ne “daya”.

Duk kasar da Allah ya albarkace ta karfin tattalin arziki, da na soji amma maimakon shugabanninta su gode wa Ubangiji, sai suka yi girman kai, suka nuna alfasha, Ubangiji ya yi alkawarin sai ya hallakar da wannan gwamnatin.

 

Da Ilimi Duk Abinda Ke Boye Ya Fito Fili

Tushen ilimi, shi ne ilimin lissafi. Lissafin gane kowane abu, musamman lissafin saba’ul masani, “euler function”, da “pi number”, kusan da su aka yi nukiliya bomb, da shi aka yi kusan komai. Da wannan lissafi, gaibu ta bayyana a sarari, babu wani abu da yake a boye yanzun, da za a ce babu wanda zai iya saninsa, sai dai Hadarar Allah, itama ya zabi wasu bayin shi, Waliyyai Rabbaniyyina.

Rabbaniyyai, ana nufin bayin Allah, kamar yadda za a ce Kanawi – Dan Kano, Sokotowi – Dan Sokoto. Su, rabbaniyyai, bincike suke yi a hadarar Allah, “Arrahman, fas’al bihi kabira”, “wattabi’i sabila man anaba ilayya”, sun son Ubangiji, sabida bincike akansa. Don haka, babu wani Annabi ko bawan Allah da zai ce, “ku zama bayi na – Kunu Ibadalli”, sai dai yace, “ku zama bayin Allah – Kunu Rabbaniyyina,” ku zama arifai ku san hadarar Allah, sai ku fahimci kaza da kaza.

Kur’ani yazo da bayanai filla-filla, ba wani abu da ya bari a baya, idan mutum ya duba Littafin “Sirril akbar”, zai ga wannan duka filla-filla, domin kur’ani yazo da shi.

Albarkar wannan ilimin lissafin, yau duk gaibu ta zama sarari. Duk abin da shekara 200 da suka shige sunan sa karya, ko kuma a ce, ba zai yiwu ba, yau ya zama gaskiya kuma ya yiwu. Ya zama gaskiya ya yiwu har ma yanzu ba wani abu da zamu ji an ce za’ayi a rika mamakin cewa, kaga ba zai yiwu ba.

Toh don haka, da ilimin Kur’anin nan, danAdam ya san asraran halitta. Cewa ba wanda ya san gaibu, idan jahili ne bashi da ilimin da zai san ta sai ya barwa Allah kayan sa. Bai hana malami yazo ya san ta ba. Malami, ba ana nufin malamin fikihu ba, da duk kan girmamashi, ana nufin Malamai masana asraran halitta, da suka hada da malaman physics, malaman binciken tarihi dake hako kasa, malaman Chemistry da sauransu. Duk wanda ya san falsafa, dole ya san akwai Allah, ko ya sani ko bai sani ba dole ya yadda da Allah, dole ya yi imani da Allah, ko ya ce bai yadda ba, toh ya yadda da wani karfi da yafi karfin halitta.Wadanda suka yi nukiliya sun fi kowa tsoran Allah, sun fi kowa tsoran kansu, sun fi kowa tsoran nukiliya, don haka suke tsawatarwa kada kowa yayi, su kuma su cigaba da yi don acigaba da jin tsoran su.

Toh, ubangiji tabaraka wata’ala da ya fadi gaibu, adali ne, haka kawai ba zai faɗmdi abu ba kuma ya cigaba da boye shi don kar a san wannan abun, ba don hakan ya fade shi ba. Ya kawo danAdam ne don ya san komai, yayi kusa da shi ta ibada, yayi kusa da shi ta ilimi, yayi kusa da shi ta ma’arifa, babu wani abu da ya kange cewa ba za’a san wannan ba.

 

Mu Fahimci Alkur’ani Da Kyau, Don Mu Iya Zama Da Zamaninmu, Kuma Mu Yi Aiki Da Kayan Zamanin

Yana daga cikin maganganun da babban Shehin Malami na wannan karnin, Mai suna Sheikh Muhammadul Shahnun, wanda ya yi akan Alkur’ani bayan ya shafe kusan shekaru 50 yana bincike kan littafin sannan ya rubuta Tafsirin Alkur’ani akan bincikensa.

Sheikh Shahnun, ya fara bincike ne duba da yadda duniyar Musulunci ke ciki a lokacinsa, wanda yake a lokacin, zamanin rikice-rikicen daular Rasha (Sobiet union) ce, inda yaga cewa, ya dace musulmai su fahimci littafinsu da gaske in ba haka ba, akwai matsala a gaba. Da wannan, Shehu Ibrahim Kaulakh ke fada cikin Diwaninsa, “Ku yi gyara, ku ajiye batun cewa, sai Mahdi ya zo, ya same ku akan kuna daidai, sai ku cigaba da tafiya tare”.

Bugu da kari, Shehu Tijjani (RA) ya fada cewa, “ina kauna ga Ubangiji ya kawo wani Namiji (Malami) da zai rairaye cunkoson abin da Malaman Fikihu su ka cusa cikin addini, ya zo mana da gangariya”.

Da yawa, suna tunanin aiki suke yi wa Shari’ar musulunci amma sun kauce hanya, “la tukaddimu baina yadayillahi wa rasulihi”, sabida ketare haddi.

Almaddah, ya yi karin haske da cewa, Mu fahimci Alkur’ani da kyau, don mu iya zama da zamanin mu lafiya, mu yi aiki da kayan zamanin mu, har ya zama ‘ya’yan kowane zamani da za su zo, za su fahimci Alkur’ani kuma su yi aiki da shi da irin kayan zamaninsu.

Sheikh Shahnun, ya fara rubuta Tafsirin Alkur’ani ne a wuraren shekarar 1990, sannan ya ce, “daga shekarar 2050, kar wanda ya kara amfani da fahimtar dake cikin Tafsirin, a yi amfani da fahimtar sabon zamani”.

Alkur'ani
Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
+ posts Bio
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da ‘Ya’yansu Alkur’ani (2)
Alkur'ani
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
Dausayin Musulunci

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

May 29, 2026
Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
Dausayin Musulunci

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

May 22, 2026
Alkur'ani
Dausayin Musulunci

Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci

May 15, 2026
Next Post
Ƴar Nijeriya Ta Rasa Lasisin Aiki A Birtaniya Bayan Gano Ta Yi Amfani Da AI A “Interview”

Ƴar Nijeriya Ta Rasa Lasisin Aiki A Birtaniya Bayan Gano Ta Yi Amfani Da AI A "Interview"

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.