Tattaunawar da ke tsakanin Amurka da Iran ta rushe bayan gaza cimma yarjejeniya kan buɗe mashigar Hormuz da kuma batun shirin nukiliyar Iran.
A makon da ya gabata, Iran ta amince da bude mashigin na tsawon makonni biyu tare da dakatar da abin da ta kira “aikin kariya,” bisa sharadin cewa hare-haren United States da Israel za su tsaya.
- Kasar Sin Ta Bukaci A Sassauta Yanayin Rikicin Iran Bayan Amurka Ta Sanya Wa Iran Din Wa’adin Cimma Yarjejeniya
- Bambancin Sin Da Amurka Bai Tsaya Kan Manufofi Kadai Ba
Sai dai tattaunawar ta ruguje bayan sa’o’i 21 na ganawa da aka gudanar a Islamabad, babban birnin Pakistan, ba tare da cimma matsaya ba.
Mataimakin shugaban Amurka, JD Vance, ya ce Iran ta ƙi amincewa da sharudan da Washington ta gabatar, yana mai cewa Amurka na buƙatar tabbaci mai ƙarfi cewa Iran ba za ta bunƙasa makaman nukiliya ba.
Har yanzu dai batutuwan mallakar iko kan mashigar Hormuz da kuma shirin nukiliyar Iran na ci gaba da zama manyan abubuwan da ke janyo saɓani tsakanin ɓangarorin biyu.















Discussion about this post